Aminiya:
2025-04-10@07:03:53 GMT

Tsohon Mataimakin Gwamnan Kogi Patrick Adaba ya rasu

Published: 10th, March 2025 GMT

Tsohon Mataimakin Gwamnan Kogi, Cif Patrick Adaba ya riga mu gidan gaskiya.

An ruwaito cewa Cif Adaba wanda ya shafe shekaru 78 a doron ƙasa ya rasu ne bayan ya yi fama da jinya a Abuja.

Abba ya ƙaddamar da bincike kan zaftare albashin ma’aikatan Kano Blatter da Platini sun sake gurfana a kotu kan zargin cin hanci

Wata majiya daga iyalansa ta ce tsohon Mataimakin Gwamnan ya rasu ne cikin daren ranar Lahadi.

Cif Patrick Adaba shi ne ya yi wa Prince Abubakar Audu mataimakin gwamna bayan samun nasara a Zaɓen 1999.

Tsohon Mataimakin Gwamnan wanda ya fito daga Ƙaramar Hukumar Adavi da ke Jihar Kogin, ƙani ne ga tsohon Darekta Janar na Hukumar Kula da Kafofin Watsa Labarai (NBC), marigayi Tom Adaba wanda ya rasu a watan jiya na Fabarairu.

Majiyar ta ce za a binne gawar marigayi Patrick Adaba a Abuja, inda aka binne yayan nasa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Hukumar NBC Jihar Kogi mataimakin gwamna Mataimakin Gwamnan

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zanga A Karkashin Jagorancin Sowore A Abuja

Jami’an ‘yansanda a gundumar Maitama da ke Abuja sun yi amfani da barkonon tsohuwa wajen tarwatsa masu zanga-zangar adawa da gwamnati, inda suka yi kira ga gwamnatin da ta dauki matakan gaggawa kan tabarbarewar tattalin arziki da kuma zargin ‘yansanda na cin zarafin al’umma a kan ikirarin dokar hana aikata laifuka ta yanar gizo. Zanga-zangar da kungiyar ‘Take-it- Back Movement’ da kungiyoyin fararen hula suka shirya a fadin kasar ya zo daidai da ranar bikin ranar ‘yansanda ta kasa a dandalin Eagle Square da ke Abuja. Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas Ya Kamata A Yi Adawa Da Kama Karya A Tabbatar Da Adalci LEADERSHIP ta tuna cewa, hukumomin ‘yansanda sun yi gargadi kan yunkurin duk wata zanga-zanga a fadin Jihohin kasar musamman ma babban birnin tarayya (FCT). Rundunar ta jaddada cewa, ranar 7 ga watan Afrilu, rana ce da gwamnatin tarayya ta ware a matsayin ranar ‘yansanda ta kasa domin murnar jajircewa da kwazon jami’ai na rundunar ‘yansandan Nijeriya. Sun yi nuni da cewa, ayyana wannan rana a matsayin ranar gudanar da zanga-zangar, akwai wata makarkashiya a ciki.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Zuba Jari Daga Kasashen Waje A Noman Zamani: Jigawa Ta Baje Kolin Aikin Noma A Abuja
  • Zulum: Boko Haram na sake kwace iko da wasu yankuna a Borno
  • Boko Haram na sake ƙwace ikon wasu yankuna a Borno — Zulum
  • Ma’aikatar Jin-ƙai ce kan gaba wajen wawure kuɗin gwamnati — Tsohon Minista
  • ɗin aikatar Jin-ƙai ce kan gaba wajen wawure kudin gwamnati — Tsohon Minista
  • Sojoji 2 Da ’Yan Ta’adda Da Dama Sun Rasu A Wani Gumurzu A Borno
  • Gwamnan Kano Ya Sadaukar Da Lambar Yabonsa Ga ‘Ya’yan Marasa Ƙarfi A Kano
  • ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zanga A Karkashin Jagorancin Sowore A Abuja
  • HOTUNA: Zanga-zangar adawa da gwamnatin Tinubu ta ɓarke a Abuja da Legas
  • Sojoji biyu da gomman ’yan ta’adda sun rasu a artabu a Borno