Aminiya:
2025-03-10@12:11:59 GMT

Ramadan: Abubuwa goma ga ma’aurata

Published: 10th, March 2025 GMT

Assalamu alaikum. Barkanmu da sake haduwa cikin wannan fili. Da fatan Allah Ya amfanar damu dukkan bayanan da za su zo cikinsa, amin.

Ga ci gaban bayani kan alherai goma ga ma’aurata cikin Ramadan.

4. Salon buɗa baki

Ma’aurata za su yi amfani da lokacin buɗa baki don ƙara kusanci, farfaɗo da shau’uka cikin zuciya da ɗumama sha’awa.

Ma’aurata su tsara buɗa bakinsu ta yadda za su zama kamar dai su sabbin masoya ne da suka sami kansu tsundum cikin sabuwar soyayyar juna.

Ramadan: Abubuwa goma ga ma’aurata Abubuwa 11 da ba a sakaci da su a Ramadan — Sheikh Daurawa

Suna buɗa bakin cikin wasa da raha da tsokanar juna, ciyar da juna a baki, kallon marmasa soyayya da kiran juna sunayen soyayya masu ƙayatarwa da sa nishaɗi.

5.Wasanni:

Don ɗebe ma juna kewa lokacin azumi, ta hanyar wasanni na baka, na jiki da kuma na wasa kwakwalwa.

Misali da Yamma lokacin da uwargida ke kakaniyar aikin gida, Maigida da iya ɗebe mata kewa da wannan wasan kacici kacicin: maigida zai ce da uwargida na fi son ki saboda kaza da kaza. Ita ma sai ta ba shi amsa, a’a nice dai na fi son ka saboda kaza da kaza.

Haka za su yi tayi wanda dalilai suka ƙare masa shi ya faɗi wasan. Bayan buɗa baku kafin lokacin tarawiyyi wasan tsere, ko tsalle ko kuma wanda yafi dace.

A kwanakin karshen mako kuma Ma’aurata su shirya ma juna kacici kacici akan wani ɓangare na ilmi, kamar akan Ramadan, Kur’ani ko tarihin Annabi Sallalahu Alayhi wa Sallam. Wanda ya ci kuma a gabatar da wata ’yar kyauta gare shi.

Waɗannan wasanni suna da matukar muhimmanci da kara karfin igiyar auren, minti goma ya yi yawa wajen aikantar da su, amma za su bar farin ciki na har abada a zuciyar Ma’aurata.

6.Ɗauke nauyi:

A dubi wani abu mai nauyi ga abokin aure sai a sauke masa wannan nauyin dan ya ji saukin Ramadan kuma a sami lada mai yawa.

Kamar wata rana Maigida ya ce uwargida ta huta, ya je ya haɗo kayan buɗa baki gaba ɗaya daga waje sai dai a zuba a ciki. Ko in uwargida ta kwashi adashenta ta canza su zuwa sababbin kuɗi ta sa ambulan ta ba Maigida ta ce ga shi ya ƙara na hidimar azumi da Sallah.

Ma’aurata dai su dubi abinda ya nauyaya ga abokin aurensu wanda sauke sa zai kawo masu saukin rayuwa sai su sauke ma shi daidai iyawarsu.

7.Sadaukarwa

Shi ne Ma’aurata su sadaukar da wani abu daga rayuwarsu dan kyautatawa ga abokin aurensu.

Kyakykyawan zamantakewar aure itace mai cike da yawan sadaukarwa ta kowane ɓangare.

Don dacewa da nun’in ladar da ke cikin Ramadan, Ma’aurata sai su aikatar da ayyukan sadaukarwa ga junansu.

Kamar maigida ya rika taya uwargida aikin gida ko ta fannin wanki da gugar kayan yara ne kawai.

Yana daga cikin Sadaukarwa kau da kai daga abubuwa marasa daďi ta ɓangaren abokin aure, kar a zarge shi game da nakasun sa da kuma yafe ma kurakurensa

8.Tunatarwa:

Sai Ma’aurata su yi nazari kan wani rauni na junansu ta ɓangaren Addini, hallayya da zamantakewa, musamman in wannan rauni da zai haifar masu da matsala a ranar hisabi, kamar rashin yin Sallah cikin lokaci, kamar yawo da zancen mutane, kamar rashin zuwa masallaci ga maigida da sauransu.

Sai a shirya nasiha da tunatarwa mai ratsa zuciya ga abokin aure akan wannan rauni nasa.

A rika nuna masa illolinsa da kuma irin halakar da za su auka da shi tun a duniya da kuma lahira.

Wannan tunatarwar za a yi ta da kalamin baki, a rubuce a takarda ko a sakon wayar tafi da gidanka.

A lura ban da zargi da ɗora laifi a cikin nasiha sai dai faɗakarwa da nusantarwa.

9.Romansiyya:

Misalan abubuwan romansiyya da Ma’aurata za su iya yi cikin Ramadan, in uwargida tana sanwa a kichin maigida ya lallaɓa ya rufe mata ido ta baya, uwargida ta rubuta wasikar soyayya ta sa a ma’ajiyar kuɗin mijinta ko a aljhunsa sai ya tafi wajen aiki ya fito da ita ya karanta.

Bayani mai lamba 5 shi ma ya shigo cikin ayyukan Romansiyya musamman wasan ‘na fi son ki saboda kaza’

10. Yin ibada tare:

Wannan shi ne mafi muhimmanci a cikin abubuwa goman da suka gabata. Ma’aurata su rika neman kusancin Allah ta hanyar yin ibadojinsu tare duk lokacin da yin hakan ta kama kuma suna waje ɗaya.

Maimakon Maigida ya yi tasbihi da yatsunshi, yana iya yi da yatsun matarsa, ita ma haka. Yin musafar Al-Qur’ani tare, ko ɗaya ya karanta ɗaya ya karanta fassarar Ayoyin.

Sai mako na gaba in sha Allah, da fatan Allah Ya sa mu kasance cikin kulawarsa a ko yaushe, amin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ma aurata Ramadan Ma aurata su uwargida ta

এছাড়াও পড়ুন:

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [2]

Shehun malami al-Imam Ibnu Juzai Allah Ya yi masa rahama, ya bayyana cewa babban dalilin da ya sa Alƙur’ani ya sauka shi ne kira ga bautar Allah da shiga cikin addininsa. Wannan magana tana da tushen ilimi mai zurfi wanda ke da nasaba da tauhidi da shari’a, da hikimar shiriya.

1. Tauhidi a Matsayin Asalin Kiran Alƙur’ani: Manufar farko da Alƙur’ani ya zo da ita; ita ce tabbatar da tauhidi, wato bautar Allah Shi kaɗai ba tare da sanya masa abokin tarayyaba. Wannan ita ce mafi girman sako da dukan annabawa suka zo da shi. Allah ya ce: “Kuma babu wani Manzo da Muka aiko a gabaninka face sai Mun yi masa wahayi cewa: Lallai babu abin bautawa da gaskiya sai Ni, to sai ku bauta mini.” Suratul Anbiya aya ta 25. Saboda haka, Alƙur’ani ya sauka ne domin ya tabbatar da cewa halitta ta san cewa akwai Mahalicci guda ɗaya, kuma Shi kaɗai ya cancanci bauta. Wannan kira yana nufin a fitar da mutane daga duhun shirka da jahilci zuwa ga hasken tauhidi da sanin Allah.

2. Shiga Cikin Addinin Allah: Manufar Alƙur’ani ta bautar Allah za ta samu ba sai a cikin addinsa. Don haka sai an shiga cikin addininsa da shari’ar da ya saukar, wato addinin Musulunci. Wannan yana nufin a bi dukan dokokin Allah da shari’o’in da suka zo a cikin Alƙur’ani da Sunnah. Allah Yana cewa: “Lalle addini a wurin Allah shi ne Musulunci.” Suratu Ãli Imrãn aya ta 19. Kuma ko mutum ya yarda da bautar Allah amma bai karɓi Musulunci ba, to Allah ba Zai karɓa masa ba, domin Ya ce:” Duk kuma wanda ya nemi bin wani addini ba Musulunci ba, to har abada ba za a karɓa daga gare shi ba, kuma shi a lahira yana cikin hasararru ” Suratu Ãli Imrãna aya ta 85. Wannan yana nuna cewa manufar Alƙur’ani ita ce shiryar da mutane su shiga cikin Musulunci ta hanyar yin imani da Allah da biyayya ga umarninsa.

3. Alƙur’ani A Matsayin Hujja: Saukar da Alƙur’ani yana ɗauke da cikakken tsarin rayuwa wanda yake jagorantar Musulumi a cikin dukan al’amuransu. Ya ƙunshi dokokin ibada kamar sallah da azumi da zakka da kuma hajji, da sauran su. Kuma ya ƙunshi dokokin mu’amala kamar ciniki da aure da kasuwanci, da sauran su. Hakanan Ya ƙunshi kyawawan ɗabi’u kamar gaskiya da zumunta, da , haƙuri da adalci da roƙon amana da sauran su. Kuma ya ƙunshi hukunce-hukunce da shari’a kamar halas da haram. Wannan yana nuna cewa saukar da Alƙur’ani ba wai kawai don sanin Allah ba ne, har ma don rayuwar duniya da lahira.

4. Manufar Saukar da Alƙur’ani ta Ķunshi dukan Halitta: Saukar da Alƙur’ani haske ne ga duniya baki ɗaya, mutane da aljanu, da ƙwari da dabbobi da halittu baki ɗaya, domin dukansu su san hanyar shiriya. Saboda haka, yana kira ga: da bin Alƙur’ani, kowa ya yi imani da Allah kaɗai ne abin bauta ba tare da an sanya masa kini ba. Mushrika da Ahlul Kitabi, wato Yahudu da Nasara da Maguzawa da kowa da kowa da su kaɗaita Allah da bauta, su shiga addininsa, kuma su bi shiriyarsa a kowane al’amari na rayuwarsu.

A taƙaice, wannan magana ta Ibnu Juzai tana bayani a kan cewa Alƙur’ani ya zo ne domin:

1. Kiran mutane su bauta wa Allah shi kaɗai,

2. Shiriyar da mutane zuwa ga addinin Musulunci,

3. Tabbatar da doka da tsarin rayuwa mai cike da adalci,

4. Fitar da mutane daga duhun jahilci zuwa hasken shiriya, domin samun jin daɗin duniya da lahira.

Wannan shi ne babban abin da Alƙur’ani ya zo da shi, kuma dukkan surori da ayoyinsa suna bayani ne akan waɗannan ginshiƙai.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [2]
  • Ramadan: Ali JC ya bai wa jama’a tallafin kayan abinci a Gombe
  • Muhimmancin Karfafa Iyali Wajen Sadaka A Watan Ramadan
  • Ramadan: Imani, Siyasa Dole Su Hadu Don Ci Gaban Kasa – Ministan Yada Labarai
  • Ramadan: Imani da Siyasa Dole Su Hadu Don Ci Gaban Kasa – Ministan Yada Labarai
  • Sojojin Isra’ila Sun Kai Hari A Kan Masallatan Nablus A Ranar Juma’ar Farko Ta Watan Ramadan
  • Ramadan: Hisbah ta rufe shagon caca a Kano
  •  Yahudawa 800 Sun Kutsa Cikin Kasar Lebanon A Yau Juma’a
  • Najeriya ta kama hanyar gyaruwa – Remi Tinubu