An haife shi a ranar 21 ga Fabrairu, 1949, kuma ya yi karatu a Jami’ar Ohio da ke Athens a Amurka, a 1981, da Jami’ar Leicester ta ƙasar Birtaniya a 1987.

 

Ya yi aiki a kamfanin jaridun New Nigerian, da hukumar talbijin ta NTA, da Ofishin Yaɗa Labarai na Amurka (USIS). Haka kuma ya yi koyarwa a Kaduna Polytechnic, ya yi aiki a Bankin Arewa da kuma Bankin Union inda a nan ya yi ritaya a ranar 26 ga Yuni, 2005.

 

A cikin saƙon ta’aziyyar sa a ranar Asabar, Minista Idris ya bayyana rasuwar Malam Kabir Ɗangogo a matsayin babban rashi ga Nijeriya da fannin sadarwa a nahiyar Afirka.

 

Ya ce: “Mutuwa ta ƙwace mana ƙwararren ma’aikaci wanda ke da cikakkiyar sadaukarwa ga aiki, da ƙwarewa a aikin jarida, da kuma gagarumar gudunmawar da ya bayar a fannin hulɗa da jama’a.

 

“Ta hanyar aikin sa, ya ɗaga martabar hulɗa da jama’a a Afirka, inda ya jagoranci ci gaba da tabbatar da ɗa’a, horar da ƙwararru, da haɗin gwiwa tsakanin ƙasashe.”

 

Ministan ya yaba wa Ɗangogo a matsayin jagora, mai hangen nesa, kuma uba ga masu aikin hulɗa da jama’a (wato public relations), wanda ya taka muhimmiyar rawa wajen inganta fannin a Nijeriya da Afrika baki ɗaya.

 

Ya ƙara da cewa a lokacin da Ɗangogo ke riƙe da muƙamin Sakatare-Janar na APRA, ya jajirce wajen ƙarfafa tattaunawa, da fito da sababbin abubuwa, da kuma ci gaba da tabbatar da ɗa’a a ɓangaren sadarwa da kula da suna.

 

Ya ce: “A madadin Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, ina miƙa ta’aziyya ta ga iyalan sa, abokan aikin sa, da ɗaukacin ‘yan jarida da masu hulɗa da jama’a.

 

“Ina roƙon Allah ya gafarta masa, ya jiƙan sa, ya kuma ba iyalan sa haƙurin jure wannan babban rashi.”

 

Ministan ya kammala da cewa gagarumar gudunmawar da Ɗangogo ya bayar za ta ci gaba da zaburar da sababbin ‘yan jarida da masu aikin hulɗa da jama’a nan gaba.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: hulɗa da jama a

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Jigawa Za Ta Rika Bayar Da Maganin Hawan Jini Da Siga Kyauta

Gwamnatin jihar Jigawa ta ce za ta bullo da shirin bada magani kyauta ga masu cutar siga da hawan jini da kuma sikila.

Kwamishinan lafiya na jihar, Dr Abdullahi Muhammad Kainuwa ya bayyana haka ga manema labarai a Dutse.

Yace tuni gwamna Umar Namadi ya bada umarnin gabatar masa da wannan kudiri domin aiwatar da shirin don kula da lafiyar al’ummar jihar musamman masu karamin karfi.

Dr Abdullahi Kainuwa yana mai cewar a yanzu haka gwamnatin jihar tana gudanar da aikin Dandamalin sabon asibitin kashi na garin Gumel kan naira miliyan 380.

A cewar sa, za a bada kwangilar sayen kayayyakin asibitin Kashi na naira miliyan dari shida.

Kwamishinan ya kara da cewar gwamnatin jihar ta kammala aikin gina dakunan wankin Koda a manyan asibitocin Dutse da Ringim da kuma Kazaure.

Yana mai cewar za a bada kwangilar sayo kayayyakin aikin dakunan domin fara wankin koda kyauta ga al’umma kafin karshen shekarar nan da muke ciki.

Dr Kainuwa, yace a yanzu haka ana wankin koda kyauta a asibitocin garuruwan Gumel da kuma Hadejia.

 

Usman Mohammed Zaria

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sharhin Bayan Labarai: Yakin Kasuwanci Tsakanin Amurka da Kasashen Duniya
  • Zuba Jari Daga Kasashen Waje A Noman Zamani: Jigawa Ta Baje Kolin Aikin Noma A Abuja
  • Jihar Kwara Za Ta Rufe Karbar Kudin Aikin Hajji A Ranar Juma’a
  • Yan Sanda A Saudiya Sun Tsare Wata Bafalasdinya Saboda Bayyana Tutar Kasarta A Kan Jakarta A Masallacin Ka’aba
  • Dan jarida Ahmad Mansour ya yi shahada bayan sojojin Isra’ila sun kona shi da ransa a Gaza
  • Hukumar Alhazai Ta Jihar Jigawa Ta Ci Gaba Da Gudanar Da Taron Bita Ga Alhazai
  • Saudiyya ta bayar da wa’adin ficewar dukkanin masu aikin Umrah daga kasar
  • Saudiyya ta sanya wa masu Umarah wa’adin ficewa daga ƙasar
  • Saudiyya ta musanta hana ’yan Nijeriya biza
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Rika Bayar Da Maganin Hawan Jini Da Siga Kyauta