Leadership News Hausa:
2025-04-10@04:21:51 GMT

Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Kano, Sun Sace Mutum Ɗaya

Published: 10th, March 2025 GMT

Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Kano, Sun Sace Mutum Ɗaya

Wasu ‘yan bindiga sun farmaki gidan Alhaji Yusha’u Ma’aruf, mamallakin wani asibiti mai zaman kansa, a garin Zakirai da ke ƙaramar hukumar Gabasawa a jihar Kano, inda suka sace wani matashi mai shekaru 20 tare da jikkata ɗan uwansa.

Rahotanni sun bayyana cewa maharan uku ɗauke da bindigogi da adduna sun afka wa gidan da misalin ƙarfe 2:15 na dare, suka sare yatsan hannun Abubakar Yusha’u mai shekaru 23 sannan suka sace ɗan uwansa, Mohammed Bello Yusha’u.

Daily Trust ta ruwaito cewa, sun kwashe wayoyi da kuɗaɗe kafin su tsere.

Tinubu Ya Buƙaci A Mayar Wa BUK Filin Rimin Zakara Da Ake Taƙaddama A Kai Ɗan Uwan Gwamnan Kano Da Malaman NNPP Sun Koma APC

Kakakin rundunar ‘yansandan Kano, Abdullahi Haruna Kiyawa, ya tabbatar da faruwar lamarin, yana mai cewa jami’an tsaro sun fara bincike don ceto wanda aka sace da kuma kamo waɗanda suka aikata harin.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Zikirai

এছাড়াও পড়ুন:

Fulham ta doke Liverpool bayan wasa 26 a jere ba tare da rashin nasara ba

Fulham ta kawo ƙarshen wasanni 26 da Liverpool ta yi a jere ba tare da rashin nasara ba a gasar Firimiyar Ingila ta wannan kakar.

Fulham ta yi nasarar doke Liverpool da 3-2 a Craven Cottage ranar Lahadi a wasan mako na 31.

Liverpool ce ta fara zura ƙwallo a ragar Fulham ta hannun Mac Allister minti 14 da fara wasa kafin Ryan Sessegnon ya rama wa Fulham a minti 23.

Fulham ba ta yi ƙasa a gwiwa ba sai da ta ƙara wa Liverpool ƙwallo ɗaya a lokacin da ɗan wasan Nijeriya, Alex Iwobi ya zura ƙwallo a ragar Liverpool a minti 32 da fara wasa.

Yayin da ake tunanin cewa Liverpool za ta iya ramawa, sai Fullham ta ƙara mata ƙwallo na uku a lokacin da Rodrigo Muniz ya zura ƙwallo a ragar Liverpool minti 37 da fara wasa.

An dai tafi hutun rabin lokaci Fullham na da rinjaye a kan Liverpool da ci 3-1 yayin da ake tunanin cewa komai na iya faruwa idan aka dawo daga hutun.

Bayan an dawo daga hutun rabin lokaci, Liverpool ta yi ta ƙoƙarin ɗaukar fansa domin ta samu ko da maki ɗaya ne daga wasan, sai dai haƙarta bai cim ma ruwa ba har sai minti 72 da fara wasa.

A minti 72 da fara wasan ne Luiz Diaz ya zura ƙwallo ɗaya a ragar Fullham lamarin da ya mayar da wasan 3-2.

Sai dai kuma Liverpool ba ta iya ƙara wa Fulham ba domin Fulham ta samu ta kare rinjayenta a wasan kuma ta cinye maki ukun wasan gaba ɗaya.

Duk da wannan sakamako, Liverpool ce ke ci gaba da jan ragama a saman teburin gasar Firimiya da maki 73 duk da cewa ba ta ƙara ratar da ta bai wa Arsenal da ke biye da ita ba.

Ita kuwa Fulham tana ta takwas a teburin gasar Firimiya inda take da maki 48.

Kociyan Liverpool, Arne Slot wanda ya ce kungiyarsa ta cancanci wannan sakamako, ya tabbatar da cewa ’yan wasansa sun tafka kura-kurai da ya zama tilas su dauki izina a kai.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan bindiga na neman N100m kafin sakin Faston da suka sace a Kaduna
  • Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Zamfara Ta Tabbatar Da Harin ‘Yan Bindiga A Banga
  • ’Yan bindiga sun mamaye garuruwa 64 a Filato — Gwamna Mutfwang
  • ’Yan bindiga sun kashe masunta 3 a Sakkwato
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Masunta 3, Sun Sace Dabbobi A Sakkwato
  • Gwamna Zulum Ya Yi Allah-wadai Da Sabbin Hare-haren Boko Haram Da Sace-sacen Mutane A Borno
  • Lakurawa Sun Kashe ’Yan Sa-kai 13 A Wani Sabon Hari A Kebbi
  • Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 4, Sun Sace 45 A Katsina
  • Mutane 2 Sun Yi Shahada A Wani Hari Da Jirgin Sama Maras Matuki Na HKI Ya Kai Wa Kasar Lebanon
  • Fulham ta doke Liverpool bayan wasa 26 a jere ba tare da rashin nasara ba