Aminiya:
2025-04-10@08:23:02 GMT

El-Rufa’i ya fice daga APC ya koma SDP

Published: 10th, March 2025 GMT

Tsohon Gwamnan Kaduna, Nasir El-Rufa’i ya tabbatar da sauya sheƙa daga jam’iyyar APC mai mulkin ƙasar zuwa jam’iyyar SDP.

Hakan na ƙunshe cikin wata sanarwa da a wallafa ranar Litinin ne a shafukansa na sada zumunta.

El-Rufai ya ce, “yanzu na yanke shawarar komawa jam’iyyar Social Democratic Party, kuma zan kasance a cikin ta wajen tafiyar da al’amurana na siyasa a nan gaba.

Kwanakin baya a lokacin tattaunawarsa da kafar talabijin ta Arise, El-Rufa’i ya bayyana cewa “jam’iyyar APC ta sauka daga kan manufofin da aka assasa ta tun fil-azal.”

Ya yi zargin cewa jam’iyyar ta gaza kiran taron shugabanninta na ƙasa tsawon shekaru, wanda ya ce hakan ya saɓa wa tanade-tanaden kundin tsarin mulkin jam’iyyar.

A yanzu dai wannan ya kawo ƙarshen raɗe-raɗin da ake yi na inda tsohon gwamnan zai nufa bayan raba gari da jam’iyyar APC.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Zamfara Ta Tabbatar Da Harin ‘Yan Bindiga A Banga

Rundunar ‘yan sandan Jihar Zamfara ta tabbatar da wani mummunan hari da ‘yan bindiga suka kai a garin Banga, da ke cikin karamar hukumar Kauran Namoda, inda aka kashe mutane biyu tare da sace wasu da dama.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sanda ta jihar, DSP Yazid Abubakar, ne ya bayyana hakan cikin wata tattaunawa ta wayar tarho da wakilinmu da ke Gusau, babban birnin jihar.

DSP Abubakar ya ce bincike na ci gaba da gudana domin gano adadin mutanen da aka sace a harin.

Ya tabbatar da cewa ana kokari don ganin an ceto mutanen da aka sace cikin koshin lafiya.

Yazid ya kara da cewa an kara kaimi wajen daukar matakan tsaro domin hana faruwar irin wannan lamari a nan gaba.

Shaidu sun shaida wa Rediyon Najeriya cewa maharan sun farmaki garin ne da misalin tsakar dare a ranar Laraba, inda suka buda wuta daga wurare da dama, lamarin da ya haifar da firgici ga mazauna garin.

Wani mazaunin garin da ya nemi a sakaya sunansa ya bayyana cewa ‘yan bindigar sun yi ta barna na tsawon sa’o’i, inda suka kashe wani dattijo da wata yarinya ‘yar shekara 18 mai suna Amina.

Ya ce da farko maharan sun sace kimanin mutane 26, amma ba su samu nasarar guduwa da su baki daya ba, sakamakon hanzarin da jami’an tsaro da ‘yan sa-kai suka yi.

Wakilinmu ya samu rahoton cewa hadin gwiwar jami’an tsaro da ‘yan sa-kai ya kai ga kashe wasu daga cikin ‘yan bindigar, yayin da wasu suka tsere da raunukan harbin bindiga. An kuma tabbatar da cewa maharan sun kasa guduwa da shanun da suka sace.

A cewar shaidu, jami’an tsaro da taimakon jiragen saman rundunar sojin saman Najeriya sun toshe hanyar da maharan ke kokarin tserewa ta kusa da kauyen Yamutsawa.

 

Daga Aminu Dalhatu

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Zamfara Ta Tabbatar Da Harin ‘Yan Bindiga A Banga
  • Mutanen da suka saba ba ni abinci yanzu na neman taimako — Obi
  • Jiragen Yaki Da Sojojin Kasa Na HKI Sun Kashe Falasdinawa 38 A Yankin Gaza Daga Safiyar Yau Zuwa Yanzu
  • Iran: Tattaunawa kai tsaye da Amurka a yanzu ba shi ne zabinmu ba
  • Nijar ta ayyana Hausa a matsayin yaren ƙasa
  • Dole Dukkanin Masu Umrah Su Fice Daga Saudiyya Kafin 29 Ga Afrilu – Hukumomi
  • Nijar ta ayyana harshen Hausa a matsayin na kasa
  • Jam’iyyar Labour Ta Yi Barazanar Dakatar Da Peter Obi Da Gwamna Otti
  • Ambaliyar ruwa ta kashe mutum 30 a Kongo
  • Kasashen Mali da Nijar da Burkina Faso sun kira jakadunsu daga Aljeriya