Aminiya:
2025-03-10@15:34:28 GMT

El-Rufa’i ya sauya sheƙa daga APC zuwa SDP

Published: 10th, March 2025 GMT

Tsohon Gwamnan Kaduna, Nasir El-Rufa’i ya tabbatar da sauya sheƙa daga jam’iyyar APC mai mulkin ƙasar zuwa jam’iyyar SDP.

Hakan na ƙunshe cikin wata sanarwa da ya wallafa ranar Litinin ne a shafukansa na sada zumunta.

’Yan bindiga sun yi garkuwa da matashi a Kano Tsohon Mataimakin Gwamnan Kogi Patrick Adaba ya rasu

El-Rufai ya ce, “yanzu na yanke shawarar komawa jam’iyyar Social Democratic Party, kuma zan kasance a cikin ta wajen tafiyar da al’amurana na siyasa a nan gaba.

Kwanakin baya a lokacin tattaunawarsa da kafar talabijin ta Arise, El-Rufa’i ya bayyana cewa “jam’iyyar APC ta sauka daga kan manufofin da aka assasa ta tun fil-azal.”

Ya yi zargin cewa jam’iyyar ta gaza kiran taron shugabanninta na ƙasa tsawon shekaru, wanda ya ce hakan ya saɓa wa tanade-tanaden kundin tsarin mulkin jam’iyyar.

A yanzu dai wannan ya kawo ƙarshen raɗe-raɗin da ake yi na inda tsohon gwamnan zai nufa bayan raba gari da jam’iyyar APC.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Kotu ta saki tsohon shugaban Koriya ta Kudu, Yoon Suk Yeol

Wata kotu a Koriya ta Kudu, ta saki tsohon shugaban ƙasar, Yoon Suk Yeol, bayan da ta yi watsi da kama shi, duk da cewa ana ci gaba da bincike kan zargin da ake masa.

Yoon, wanda aka dakatar daga mulki, an tsare shi ne tun a watan Janairu bayan da ake zarginsa da ƙoƙarin kifar da mulkin farar hula.

Ramadan: Hisbah ta rufe shagon caca a Kano An kashe shugaban Lakurawa, Maigemu a Kebbi

A ranar 3 ga watan Disamban 2024, jami’an tsaro sun kai masa samame bisa zargin tayar da zaune tsaye.

Bayan an sake shi, Yoon ya fito daga gidan yari yana murmushi, sannan ya sunkuyar da kai domin nuna godiya ga magoya bayansa da suka zo ganinsa.

A ranar Juma’a, kotu ta soke umarnin da aka bayar na kama shi, inda ta ce babu isassun hujjoji da ke tabbatar da laifin da ake zarginsa da shi.

Duk da haka, ana ci gaba da shari’a kan batun tsige shi daga mulki.

Masu gabatar da ƙara sun ce za su mayar da hankali kan gabatar da hujjoji a gaban kotu maimakon ɗaukaka ƙara kan sakinsa.

Idan har kotun tsarin mulki ta tabbatar da tsige shi, Koriya ta Kudu dole ne ta gudanar da sabon zaɓen shugaban ƙasa cikin kwanaki 60.

Duk da haka, ana sa ran za a ci gaba da shari’ar Yoon, ko da kuwa an sauke shi daga mulki gaba ɗaya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Abin da ya sa na sauya sheƙa daga APC zuwa SDP — El-Rufai
  • El-Rufa’i ya fice daga APC ya koma SDP
  • Tsohon Gwamnan Kaduna El-Rufai Ya Koma SDP
  • Tsohon Mataimakin Gwamnan Kogi Patrick Adaba ya rasu
  • PDP ta sake ɗage babban taronta zuwa Mayun 2025
  • An samu tsohon shugaban hukumar tsaron Faransa da zamba
  • Tsohon shugaban hukumar tsaron Faransa na fuskantar zargin zamba
  • Kotu ta saki tsohon shugaban Koriya ta Kudu, Yoon Suk Yeol
  • Jigon APC Ya Fara Yunkurin Sulhunta Kwankwaso, Ganduje Da Shekarau