Aminiya:
2025-03-10@15:33:16 GMT

Abin da ya sa na sauya sheƙa daga APC zuwa SDP — El-Rufai

Published: 10th, March 2025 GMT

Tsohon Gwamnan Kaduna, Nasir El-Rufa’i ya tabbatar da sauya sheƙa daga jam’iyyar APC mai mulkin ƙasar zuwa jam’iyyar SDP.

Hakan na ƙunshe cikin wata sanarwa da ya wallafa ranar Litinin ne a shafukansa na sada zumunta.

’Yan bindiga sun yi garkuwa da matashi a Kano Tsohon Mataimakin Gwamnan Kogi Patrick Adaba ya rasu

El-Rufai ya ce, “yanzu na yanke shawarar komawa jam’iyyar Social Democratic Party, kuma zan kasance a cikin ta wajen tafiyar da al’amurana na siyasa a nan gaba.

Ya ce a matsayinsa na wanda aka kafa jam’iyyar APC da shi, zai ci gaba da tunawa da faɗi tashi da kuma kyakkyawar mu’amalar da ya yi da duk abokan hulɗarsa.

Ya ce ya yi fatan cewa jam’iyyar APC wadda da shi aka kafa ta tun a shekarar 2013 za ta tsaya a kan tubalin da suka assasa ta har zuwa lokacin da zai yi ritaya daga siyasa.

Sai dai ya ce a tsawon shekaru biyu da suka gabata, ya lura cewa akwai halin ko-in-kula gami da sauka daga kan tsari da aƙida a ɓangaren waɗanda ke riƙe da madafan ikon jam’iyyar a yanzu, da ba su da burin magance matsalolin da suka addabi jam’iyyar.

Ya ce a nasa ɓangaren, ya bayyana damuwa a cikin sirri da kuma kwanan a bainar jama’a game da halin da jam’iyyar take ciki, amma ya ga babu mafita face ficewa daga jam’iyyar domin sauya sheƙa zuwa wata da zai ci gaba da gudanar da al’amuran siyasa da zai kawo ci gaba a Jihar Kaduna, Arewa da kuma Nijeriya baki ɗaya.

“A matsayina na ɗan jam’iyya mai kishi, na yi aiki wajen taimaka wa jam’iyyar APC ta samun nasara a zaɓukan 2015, 2019 da 2023.

“Ina ɗaya daga cikin gwamnoni da dama da aka zaɓa a ƙarƙashin inuwar jam’iyyar a 2015 da 2019, waɗanda suka tsaya tsayin daka wajen tabbatar da dimokuradiyya da ka’idojin ciyar da ƙasa gaba.

“Tsawon shekaru takwas da na yi a matsayin Gwamnan Jihar Kaduna, na duƙufa wajen aiwatar da tsare-tsare masu inganci don ciyar da al’umma gaba a fannin ilimi da kiwon lafiya, da faɗaɗa ababen more rayuwa, samar da ayyukan yi da jawo jari.

“Waɗannan bayanan kaɗan ne a cikin manufofin da jam’iyyar APC mai ci ta yi watsi da su a yanzu tare da wulaƙanta mambobinta a shekaru biyu da suka gabata. Na ga abin ba mai karɓuwa ba ne.

“A yau 10 ga Maris, 2025, na miƙa takardar barin jam’iyyar APC a mazaɓata ta Kaduna.

“Sai dai kafin ɗaukar wannan matakin, na kammala tuntuɓar mashawarta, abokan aiki da magoya baya a duk faɗin ƙasar game da hakan.

“A yanzu na yanke shawarar shiga jam’iyyar Social Democratic Party (SDP), kuma na ɗauke ta a matsayin inuwar gudanar da harkokina na siyasa da sauran ayyuka.

“Saboda haka, zan mayar da hankali wajen yin cuɗanya tare da jawo hankalin sauran ’yan jam’iyyun adawa su shigo cikinmu, mu taru a karkashin tsarin dimokuraɗiyya bai ɗaya domin ƙalubalantar jam’iyyar APC a duk wani zaɓe da zaɓen fidda gwani da za a yi daga yanzu zuwa 2027 da yardar Allah.

“Don haka ina kira ga dukkan magoya bayanmu da sauran waɗanda suka damu da makomar ƙasarmu da su shigo jam’iyyar SDP don ganin Nijeriya ta bunƙasa a matsayin abin alfahari ga ‘yan Afirka da duk wani baƙar fata.”

Ana iya tuna cewa tun a kwanakin baya yayin tattaunawarsa da gidan talabijin na Arise, El-Rufa’i ya bayyana cewa “jam’iyyar APC ta sauka daga kan manufofin da aka assasa ta tun fil-azal.”

Ya yi zargin cewa jam’iyyar ta gaza kiran taron shugabanninta na ƙasa tsawon shekaru, wanda ya ce hakan ya saɓa wa tanade-tanaden kundin tsarin mulkin jam’iyyar.

A yanzu dai wannan ya kawo ƙarshen raɗe-raɗin da ake yi na inda tsohon gwamnan zai nufa bayan raba gari da jam’iyyar APC.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: jam iyyar APC jam iyyar A jam iyyar a

এছাড়াও পড়ুন:

 Syria: Kungiyoyi Masu Dauke Da Makamai Suna Ci Gaba Da  Kai Wa Kauyukan Lazikiyya Da Tartus Hare-hare

Tashar talbijin din ‘almayadin’ mai watsa shirye-shirye daga Lebanon ta ambaci cewa; Wasu kauyuka na mabiya mazhabar Alawiyya dake Tartus, da kuma Lazikiyya, sun fuskanci hare-hare daga masu dauke da makamai.

A yau Lahadi, masu dauke da makaman sun kutsa cikin wasu kauyukan Ramilah, Naq’a dake kusa da Jabalah.

Daga jiya zuwa yau masu dauke da makaman sun yi kisan kiyashi a wurare  fiye da 10.

Majiyar Almayadin ta ce ya zuwa yanzu adadin wadanda aka kashe bisa bangaranci sun kai 1000.

Sai dai kuma tshohon mai bai wa shugaban majalisar ‘yan Alawiyya shawara Muhammad Nasir, ya ce, adadin wadanda aka kashe din sun kai 1,700.

Hare-haren sun hada da kona kauyuka 6 a yankin gabar ruwan Midtreniya na kasar Syria.

Da akwai wasu daruruwan gawawwaki a kwance akan titunan garuruwa da kauyuka da biranen yakin Lazikiyya da Hasakah.

A cikin wasu kauyukan mutane da dama sun gudu zuwa kan duwatsu da dajuka domin su tsira da rayukansu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An cafke mutum uku kan satar wayoyin lantarki a Adamawa
  • El-Rufa’i ya sauya sheƙa daga APC zuwa SDP
  • El-Rufa’i ya fice daga APC ya koma SDP
  • Tsohon Gwamnan Kaduna El-Rufai Ya Koma SDP
  • Isra’ila ta aike da tawaga zuwa Doha domin ci gaba da tattaunawar sulhun Gaza
  • PDP ta sake ɗage babban taronta zuwa Mayun 2025
  •  Syria: Kungiyoyi Masu Dauke Da Makamai Suna Ci Gaba Da  Kai Wa Kauyukan Lazikiyya Da Tartus Hare-hare
  • Tashe-tashen Hankula Na Ci Gaba Da Yin Sanadin Rayuka A Siriya
  • ‘Yansanda A Legas Sun Kama Mutum 35 Da Ake Zargi Da Fashi Cikin Mako Guda