Aminiya:
2025-04-10@04:24:28 GMT

An cafke mutum uku kan satar wayoyin lantarki a Adamawa

Published: 10th, March 2025 GMT

’Yan sanda sun cafke wasu mutum uku bisa zargin lalatawa da kuma satar wayoyin lantarki a ƙauyen Bororo da ke Ƙaramar Hukumar Michika ta Jihar Adamawa.

An cafke ababen zargin ne da wayoyin lantarkin yayin wani sintiri da jami’an ’yan sanda suka gudanar a ranar 9 ga wannan wata na Maris.

Abin da ya sa na sauya sheƙa daga APC zuwa SDP — El-Rufai ’Yan bindiga sun yi garkuwa da matashi a Kano

Mai magana da yawun rundunar ’yan sandan, Suleiman Yahaya Nguroje, ya ce ababen zargin da ke hannu sun yi iƙirarin aikata laifin da ake zarginsu da shi.

Sai dai ya ce za a ci gaba da gudanar da bincike gabanin ɗaukar matakin da ya ce nan gaba kaɗan.

Kwamishinan ’yan sandan jihar, Dankombo Morris, ya yaba wa jami’an da suka yi ruwa da tsaki wajen cafke ababen zargin, yana mai jaddada aniyar ƙara ƙaimi wajen tsare dukiyoyin al’umma.

Rundunar ’yan sandan ta buƙaci mazauna da su ci gaba da ba ta haɗin kai wajen lura da duk wani motsi tare da kai rahoto duk wani abin zargi zuwa mahukunta mafi kusa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda Jihar Adamawa Wayoyin Lantarki

এছাড়াও পড়ুন:

Najeriya: An gudanar da zanga-zangar adawa da wasu shirye-shiryen  gwamnati

An gudanar da zanga-zangar adawa da gwamnatin Shugaba Bola Tinubu wada ta barke a wasu manyan biranen Nijeriya da suka haɗa da Abuja da Legas da kuma Fatakwal.

Zanga-zangar wadda wata kungiyar gwagwarmaya ta Take It Back ta shirya na gudana ne duk da gargadin da ’yan sanda suka yi na neman a jingine ta.

A Abuja, babban birnin Nijeriya, fitaccen dan gwagwarmaya, Omoyele Sowore da lauyan nan mai kare hakkin bil Adama, Deji Adeyanju ne ke jagorantar zanga-zangar duk da yunkurin ’yan sanda na hana su rawar gaban hantsi

An kuma hangi masu zanga-zangar ɗauke da alluna da kwalaye masu dauke da rubutun bayyana buƙatunsu a wasu hanyoyi da ke Ikeja, babban birnin Jihar Legas.

A Jihar Ribas kuma, masu zanga-zangar sun yi dandazo a filin Isaac Boro da ke birnin Fatakwal, amma dai ’yan sanda sun rika harba musu barkonon tsohuwa domin daƙile manufar da suka fito ita.

Kungiyar ta Take It Back na cewa babu gudu babu ja da baya domin nuna adawa da dokar ta-baci da aka sanya a Jihar Ribas da kuma abin da ta kira cin zarafin bil’adama da kuma amfani da dokar ta’addancin yanar gizo ba bisa ka’ida ba.

Wannan dai na zuwa ne a yayin da rundunar ‘yan sandan Nijeriya ta gargaɗi masu shirin zanga-zangar a ranar Litinin 7 ga watan Afrilu a faɗin kasar su sake tunani domin a ranar ce ‘yan sandan kasar suke bukukuwa domin nuna gudunmawar da suka bayar don ci-gaban Nijeriya.

Rundunar ta ce zanga-zangar tana zuwa ne a lokacin da bai dace a yi zanga-zanga a kasar ba.

Wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan kasar, Olumuyiwa Adejobi, ya fitar ta ce rundunar ba ta adawa da ‘yancin ‘yan kasar na taruwa da yin gangami da Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya ya ba su.

Sai dai kuma sanarwar ta ce rundunar na fargaba game da burin wadanda suka shirya yin zanga-zangar rana daya da ranar da aka ware domin yaba wa irin jajircewa da sadaukar da kai na ‘yan sandan Nijeriya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Zamfara Ta Tabbatar Da Harin ‘Yan Bindiga A Banga
  • Mutanen da suka saba ba ni abinci yanzu na neman taimako — Obi
  • Jiragen Yaki Da Sojojin Kasa Na HKI Sun Kashe Falasdinawa 38 A Yankin Gaza Daga Safiyar Yau Zuwa Yanzu
  • Hatsarin Mota Ya Yi Ajalin Mutum 5 A Yobe
  • ‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Satar Mota A Bauchi
  • Ma’aikatar Jin-ƙai ce kan gaba wajen wawure kuɗin gwamnati — Tsohon Minista
  • ɗin aikatar Jin-ƙai ce kan gaba wajen wawure kudin gwamnati — Tsohon Minista
  • HKI Ta Kara Yawan Hare-Hare A Kan Gaza A Dai Dai Lokacinda Ake Kiranta Zuwa Tsagaita Wuta
  • Najeriya: An gudanar da zanga-zangar adawa da wasu shirye-shiryen  gwamnati
  • Kasar Sin Ta Nanata Kudurinta Na Ci Gaba Da Bude Kofa Yayin Wani Taro Da Kamfanonin Amurka