Ko dai Gwamna Fubara ya yi murabus ko a tsige shi — APC
Published: 10th, March 2025 GMT
Jam’iyyar APC ta yi kira ga Gwamnan Ribas, Siminalayi Fubara da ya sauka daga mulki ko kuma a tsige shi.
Shugaban APC na Jihar Ribas, Tony Okocha ne ya bayyana haka yayin zantawa da manema labarai yau Litinin a birnin Fatakwal.
An cafke mutum uku kan satar wayoyin lantarki a Adamawa Abin da ya sa na sauya sheƙa daga APC zuwa SDP — El-RufaiOkocha ya ce gayyatar da Fubara ya aika wa ’yan majalisar dokokin jihar domin ya gana da su akwai lauje cikin naɗi.
“Hukuncin Kotun Ƙoli ne ƙarshe babu wani abu da wani zai iya yi. Abun da ya rage wa gwamnan shi ne ko dai ya sauka, ko kuma a tsige shi,” in ji Okocha.
Tun da farko, bayan hukuncin kotun ƙolin, majalisar jihar ta ba gwamnan jihar wa’adin kwana biyu ya sake gabatar da kasafin kuɗi, gayyatar da ya ƙi amsawa.
Daga baya shi kuma gwamnan ya gayyace su gidan gwamnati domin su tattauna, inda su ma suka ce ba za su je ba, domin a kafofin sadarwa suka ga gayyatar.
Ana iya tuna cewa, majalisar ta kuma bai wa Gwamna Fubara wa’adin sallamar da sau naɗe-naɗen da ya yi wanda ba ita ta tantance su ba.
Za a sake zaɓen ƙananan hukumomin Ribas
A makon jiya ne Hukumar zaɓen Rivers ta saka 9 ga watan Agusta a matsayin ranar sake zaɓen ƙananan hukumomi.
Rahotonni sun ambato shugaban hukumar Adolphus Enebeli na sanar da hakan yayin wata ganawa da masu ruwa da tsaki a birnin Fatakwal.
Wannan na zuwa ne bayan Kotun Ƙolin Nijeriya ta soke zaɓen da hukumar ta gudanar a ranar 5 ga watan Oktoban 2024.
A gefe guda kuma, majalisar dokokin jihar ta gayyaci shugaban hukumar ya bayyana a gabanta domin yin bayani game da zaɓen.
Wannan dambarwar na zuwa ne a yayin da rikicin siyasa tsakanin gwamnan da tsohon gwamna kuma Ministan Abuja, Nyesom Wike, ke ƙara kamari.
Tun bayan ɗarewar Fubara kan mulki, dangantakar da ke tsakaninsa da magabacinsa ta yi tsami, lamarin da ya haddasa rabuwar kawuna a Majalisar Dokokin jihar.
Wasu ‘yan majalisa sun tsaya tsayin daka domin kare gwamnan, yayin da wasu ke goyon bayan APC da Wike.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Jihar Ribas Siminalayi Fubara
এছাড়াও পড়ুন:
Kisan Isuhu Yellow: ’Yan bindiga sun kai harin ɗaukar fansa
Wasu ’yan bindiga a ranar Lahadin da ta gabata sun kai harin ɗaukar fansar kashe ƙasurgumin ɗan ta’addan nan, Kachalla Isuhu Yellow da aka fi sani da Ɗan Isuhu.
’Yan ta’addan sun kai harin ne ƙauyen Keta da ke Ƙaramar Hukumar Tsafe ta Jihar Zamfara, domin ɗaukar fansar kashe jagoransu da jami’an tsaro suka yi makonni biyu da suka gabata.
Kotu ta daure ango wata 6 saboda likin kudi a bikinsa Gaza: Isra’ila ta kashe Falasdinawa 58 a awa 58Mazauna sun ce maharan sun kashe mutum ɗaya yayin da suka ƙone motoci 11 sannan kuma suka wawushe kayayyaki a kantinan ’yan kasuwa a yayin harin.
Bayanai sun ce ana zargin ’yan ta’addan da suka kai wannan hari mayaƙan Adamu Aliero ne — yayan marigayi Ɗan Isuhu.
Kachalla Yellow wanda ake alaƙantawa da kai munanan hare-hare a Zamfara da kuma babbar hanyar Funtua zuwa Gusau, ya gamu da ƙarshensa ne a yayin wani artabu da wata rundunar haɗin gwiwa ta Asakarawan Zamfara da kuma jami’an ’yan sanda a ƙauyen Keta.
A yayin da wasu rahotanni ke cewa, Ɗan Isuhu ya yi gamo da ƙarshensa ne a hannun wasu ’yan ta’adda masu adawa da shi da ke yi wa Dogo Gide mubaya’a, wasu kuma na cewa dakarun soji ne suka kawar da shi daga doron ƙasa.
Wani mazauni Danjigba — wani yanki da ke makwabtaka da Keta — ya tabbatar da cewa an kashe Isuhu Yellow ne a yayin da yake yunƙurin yi wa jami’an tsaro kwanton ɓauna a hanyarsu ta zuwa ƙauyen Keta domin kai ɗauki.
“Shi da mayaƙansa sun yi ƙoƙarin yi wa jami’an tsaron kwanton ɓauna amma a yayin musayar wuta da su aka kashe shi tare da mayaƙansa da dama.”
Ya ƙara da cewa, ragowar ’yan ta’adda a hanyarsu ta tserewa sun kai wa mazauna Danjigba hari, inda suka kashe mutum takwas ciki har da wani ɗan uwansa da wawushe kuɗi a hannun ’yan kasuwa.
Duk da aukuwar wannan hari, sai dai mazauna suka yi murnar mutuwar Isuhu Yellow, suna masu bayyana shi a matsayin marar imani wanda ya ɗauki alhakin sacewa da zubar da jinin mutane da dama a Tsafe, Gusau, Dan Sadau da kuma Funtua.
Kakakin rundunar ’yan sandan Zamfara, DSP Yazid Abubakar, ya tabbatar da kashe Isuhu Yellow a wani aikin haɗin gwiwa na jami’an tsaro da suka daƙile harin da aka kai ƙauyen Keta.