Ko dai Gwamna Fubara ya yi murabus ko a tsige shi — APC
Published: 10th, March 2025 GMT
Jam’iyyar APC ta yi kira ga Gwamnan Ribas, Siminalayi Fubara da ya sauka daga mulki ko kuma a tsige shi.
Shugaban APC na Jihar Ribas, Tony Okocha ne ya bayyana haka yayin zantawa da manema labarai yau Litinin a birnin Fatakwal.
An cafke mutum uku kan satar wayoyin lantarki a Adamawa Abin da ya sa na sauya sheƙa daga APC zuwa SDP — El-RufaiOkocha ya ce gayyatar da Fubara ya aika wa ’yan majalisar dokokin jihar domin ya gana da su akwai lauje cikin naɗi.
“Hukuncin Kotun Ƙoli ne ƙarshe babu wani abu da wani zai iya yi. Abun da ya rage wa gwamnan shi ne ko dai ya sauka, ko kuma a tsige shi,” in ji Okocha.
Tun da farko, bayan hukuncin kotun ƙolin, majalisar jihar ta ba gwamnan jihar wa’adin kwana biyu ya sake gabatar da kasafin kuɗi, gayyatar da ya ƙi amsawa.
Daga baya shi kuma gwamnan ya gayyace su gidan gwamnati domin su tattauna, inda su ma suka ce ba za su je ba, domin a kafofin sadarwa suka ga gayyatar.
Ana iya tuna cewa, majalisar ta kuma bai wa Gwamna Fubara wa’adin sallamar da sau naɗe-naɗen da ya yi wanda ba ita ta tantance su ba.
Za a sake zaɓen ƙananan hukumomin Ribas
A makon jiya ne Hukumar zaɓen Rivers ta saka 9 ga watan Agusta a matsayin ranar sake zaɓen ƙananan hukumomi.
Rahotonni sun ambato shugaban hukumar Adolphus Enebeli na sanar da hakan yayin wata ganawa da masu ruwa da tsaki a birnin Fatakwal.
Wannan na zuwa ne bayan Kotun Ƙolin Nijeriya ta soke zaɓen da hukumar ta gudanar a ranar 5 ga watan Oktoban 2024.
A gefe guda kuma, majalisar dokokin jihar ta gayyaci shugaban hukumar ya bayyana a gabanta domin yin bayani game da zaɓen.
Wannan dambarwar na zuwa ne a yayin da rikicin siyasa tsakanin gwamnan da tsohon gwamna kuma Ministan Abuja, Nyesom Wike, ke ƙara kamari.
Tun bayan ɗarewar Fubara kan mulki, dangantakar da ke tsakaninsa da magabacinsa ta yi tsami, lamarin da ya haddasa rabuwar kawuna a Majalisar Dokokin jihar.
Wasu ‘yan majalisa sun tsaya tsayin daka domin kare gwamnan, yayin da wasu ke goyon bayan APC da Wike.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Jihar Ribas Siminalayi Fubara
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaban Majalisar Ƙoli ta Shari’ar Musulunci a Najeriya ya rasu
Allah Ya yi wa Shugaban Majalisar Ƙoli ta Shari’ar Muslunci a Najeriya, Sheikh Abdul Rasheed Hadiyatullah, rasuwa.
Babban Mufti na ƙasar Yarbawa, Sheikh Daood Imran Molaasan, ne ya sanar da rasuwar Sheikh Abdul Rasheed Hadiyatullah a cikin wata sanarwa da ya sanya hannu a kai a daren Litinin.
Sai dai bai bayar da cikakken bayani game da inda Sheikh Hadiyatullah ya rasu ko kuma lokacin da hakan ya faru ba.
Sheikh Molaasan ya bayyana cewa rasuwar marigayi Sheikh Hadiyatullah ta bar giɓi mai wuyar cikewa a shugabancin Musulunci na ƙasar.
Bom ɗin Boko Haram ya kashe mutane 26 a Borno NAJERIYA A YAU: Dalilin karyewar farashin shinkafa a kasuwannin Najeriya“An haife shi a garin Iwo a Jihar Osun kuma an san shi da dabi’u Musulunci. Sheikh Hadiyatullah ya kasance fitaccen malamin Musulunci kuma masanin shari’a, wanda an san shi da ƙoƙarinsa na neman a aiwatar da Shari’a Musulunci a tsarin mulkin Najeriya, tattaunawa tsakanin addinai, da zaman lafiya a tsakanin al’ummomin Najeriya masu bambancin addini.
“Ya yi aiki a matsayin Shugaban Majalisar Shari’ar Musulunci na tsawon shekaru, inda ya jagorance ta a lokutan ƙalubalen zamantakewa da ci gaba.
“Sheikh Hadiyatullah ya fara karatun addinin Musulunci a wurin malaman gida kafin ya ci gaba da karatunsa a ƙasashen waje.
“Ya samu girmamawa a faɗin Najeriya da ma wajenta saboda zurfin ilminsa a fannin fiƙihun Musulunci da kuma salon shugabancinsa mai nutsuwa da tsayin daka kan akida,” kamar yadda Molaasan ya bayyana.
Ya kuma yi addu’ar Allah ya gafarta wa Sheikh Hadiyatullah ya kuma ba shi Aljannatul Firdaus.