Gwamnatin Kano Ta Bullo Da Sabbin Hanyoyin Kare Makarantunta Daga Kalubalen Tsaro
Published: 10th, March 2025 GMT
Gwamna Abba Kabir Yusuf na jihar Kano ya ce gwamnatinsa ta dauki wani muhimmin mataki na tabbatar da tsaron makarantunta, inda za a hada hannu da masu ruwa da tsaki don kara karfafa tsaro a yankunan da makarantu suke.
Gwamna Abba Kabir Yusuf ya bayyana hakan ne a yayin bikin bude taron masu ruwa da tsaki kan harkar tsaro a jihar da kuma horas da jami’an tsaron makarantu, wanda aka gudanar a fadar gwamnatin jihar.
Gwamnan wanda kwamishinan Ilimi Alhaji Ali Haruna Makoda ya wakilta, ya tabbatar wa masu ruwa da tsaki kudirin gwamnatinsa na bunkasa fannin ilimi a jihar.
Ya ce yayin da Najeriya ke ci gaba da fuskantar kalubale wajen tabbatar da tsaro a makarantu, wannan shirin wani muhimmin mataki ne na karfafa tsaro da inganta yanayin koyo.
A jawabinsa, kwamishinan ‘yan sandan jihar, Abayomi Shogunle, ya jaddada muhimmancin tsaro a makarantun, inda ya bayyana cewa abu ne da gwamnati mai ci ta ba da fifikoa kai.
Ya yi nuni da cewa, Sifeto janarna ‘yan sanda ne ya kaddamar da rundunar tsaro ta makarantu da nufin magance matsalolin tsaro a makarantun firamare da sakandare da manyan makarantu.
Shi ma a nasa jawabin mataimakin shugaban jami’ar Aliko Dangote, Farfesa Musa Tukur Yakasai, ya yabawa horon kan inganta tsaro a cibiyoyin ilimi.
Tun da farko Sufeto Janar na ‘yan sanda Kayode Egbetokun, wanda mataimakin sufeto janar shiyya ta daya AIG Ahmad Ammani ya wakilta, ya jaddada muhimmancin hada hannu tsakanin jama’a da jami’an tsaro domin magance matsalar rashin tsaro a makarantu da cibiyoyi.
Taron mai taken “Karfafa Tsaro da Hadin Kan Al’umma wajen Kare Ilimi,” ya hada wakilai daga ‘Yan sandan Najeriya, da rundunar Soji, da cibiyoyin ilimi da dai sauransu.
Taron ya samu halartar shugabannin hukumomin tsaro na Kano da sauran masu ruwa da tsaki.
Abdullahi Jalaluddeen
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Makarantu Tsaro masu ruwa da tsaki tsaro a makarantu
এছাড়াও পড়ুন:
Abba ya ƙaddamar da bincike kan zaftare albashin ma’aikatan Kano
Gwamnan Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya yi tsattsauran gargaɗi dangane da rahotannin da ke yawo kan cirar kuɗi daga albashin ma’aikatan gwamnati ko kuma ƙin biyan su gaba ɗaya.
Ya bayyana hakan a matsayin cin zarafin ma’aikata da cin amanar jama’a, yana mai jaddada cewa gwamnatinsa ba za ta lamunci hakan ba.
Blatter da Platini sun sake gurfana a kotu kan zargin cin hanci NAJERIYA A YAU: Ladan Da Mai Aikin Ƙarfi Yake Samu A Lokacin AzumiBiyo bayan korafe-korafen da ma’aikata suka yi, na cewa wasu daga cikinsu sun shafe watanni ba tare da samun hakkokinsu ba, Gwamna Yusuf ya sha alwashin gano masu hannu a wannan ɗanyen aiki da kuma hukunta su.
“Gwamnatin nan ba za ta yarda da zalunci ma’aikatanta ba. Duk wanda aka samu da hannu a wannan mummunan aiki zai fuskanci hukunci mai tsanani,” in ji Gwamnan.
Gwamnan ya kafa kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin matsalar, wanda zai gudanar da cikakken bincike kan tsarin biyan albashi daga watan Oktoba 2024 zuwa Fabrairu 2025
An ɗora wa kwamitin alhakin gano ma’aikatan da abin ya shafa, tasirin hakan kan kuɗin gwamnati, tare da ba da shawarwari kan yadda za a magance matsalar da kuma hukunta masu hannu a ciki.
Kwamitin, wanda ke da mambobi bakwai yana karkashin jagorancin Kwamishinan Raya Karkara da Ci-gaban Al’umma kuma tsohon Akanta Janar na Jiha, Abdulkadir Abdussalam.
Mambobin sun hada da: – Abdulkadir Abdussalam – Shugaban Kwamitin kuma Kwamishinan Raya Karkara da Ci-gaban Al’umma da Dokta Bashir Abdu Muzakkari – Mai ba da shawara na musamman kan tattalin arzikin zamani.
Sai Dokta Aliyu Isa Aliyu – Darakta Janar na Hukumar Kididdiga ta Jihar Kano da Dokta Hamisu Sadi Ali – Darakta Janar na Hukumar Kula da Bashin Jihar Kano da Hajiya Zainab Abdulkadir – Darakta ta Cibiyar Kwamfuta ta Jihar Kano.
Akwai kuma Aliyu Muhammad Sani – Darakta na Bincike da Tantancewa a Ofishin Sakataren Gwamnati da Ummulkulthum Ladan Kailani – Mataimakiyar Sakatariya, Ofishin Sakataren Gwamnati.
An bai wa kwamitin wa’adin kwanaki bakwai domin kammala binciken tare da mika rahoto wanda zai ƙunshi sunayen masu laifi, asarar da aka yi, da kuma shawarwarin magance matsalar gaba ɗaya.