Gwamna Abba Kabir Yusuf na jihar Kano ya ce gwamnatinsa ta dauki wani muhimmin mataki na tabbatar da tsaron makarantunta, inda za a hada hannu da masu ruwa da tsaki  don kara karfafa tsaro a yankunan da makarantu suke.

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya bayyana hakan ne a yayin bikin bude taron masu ruwa da tsaki kan harkar tsaro a jihar  da kuma horas da jami’an tsaron makarantu, wanda aka gudanar a fadar gwamnatin jihar.

Gwamnan wanda kwamishinan Ilimi Alhaji Ali Haruna Makoda ya wakilta, ya tabbatar wa masu ruwa da tsaki  kudirin gwamnatinsa na bunkasa fannin ilimi a jihar.

Ya ce yayin da Najeriya ke ci gaba da fuskantar kalubale wajen tabbatar da tsaro a makarantu, wannan shirin wani muhimmin mataki ne na karfafa tsaro da inganta yanayin koyo.

A jawabinsa, kwamishinan ‘yan sandan jihar, Abayomi Shogunle, ya jaddada muhimmancin tsaro a makarantun, inda ya bayyana cewa abu ne da  gwamnati mai ci ta ba da fifikoa kai.

Ya yi nuni da cewa, Sifeto janarna ‘yan sanda ne ya kaddamar da rundunar tsaro ta makarantu da nufin magance matsalolin tsaro a makarantun firamare da sakandare da manyan makarantu.

Shi ma a nasa jawabin mataimakin shugaban jami’ar Aliko Dangote, Farfesa Musa Tukur Yakasai, ya yabawa horon kan  inganta tsaro a cibiyoyin ilimi.

Tun da farko Sufeto Janar na ‘yan sanda Kayode Egbetokun, wanda mataimakin sufeto janar shiyya ta daya AIG Ahmad Ammani ya wakilta, ya jaddada muhimmancin hada hannu tsakanin jama’a da jami’an tsaro domin magance matsalar rashin tsaro a makarantu da cibiyoyi.

Taron mai taken “Karfafa Tsaro da Hadin Kan Al’umma wajen Kare Ilimi,” ya hada wakilai daga ‘Yan sandan Najeriya, da rundunar Soji, da cibiyoyin ilimi da dai sauransu.

Taron ya samu halartar shugabannin hukumomin tsaro na Kano da sauran masu ruwa da tsaki.

Abdullahi Jalaluddeen

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Makarantu Tsaro masu ruwa da tsaki tsaro a makarantu

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Kasar Aljeriya Ta Dakatar Da Zirga-Zirgan Jiragen Saman Kasar Zuwa Kasar Mali

Gwamnatin kasar Aljeriya ta dakatar da duk zirga-zirgin jiragen sama daga kasar Mali da kuma zuwa kasar saboda abinda ta kira keta hurumin sararin samaniyar kasar.

Shafin yanar giza na watsa labarai “Africa News” ya nakalto tashar talabijin ta kasar Aljeriya na fadar haka a daren Lahadi.

Kafin haka dai matsalolin sun tashi tsakanin kasashe yanken Sahel 3 Niger,  Mali da Burkiya faso kan kakkabo jirgin saman yaki wanda bai da matuki wanda ya keta sararin samar kasar ta Aljeriya a makon da ya gabata, wanda ya sa kasashen uku suka janye jakadunsu daga kasar.

Gwamnatin kasar Mali dai bata yi magana a kan wannan matakin da gwamnatin kasar ta Aljeriya ta dauka ba.

Sai dai dakatar da zirga-zirgan jiragen sama tsakanin kasashen biyu zai shafi al’amuran kasuwanci soai a kasashen yankin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 10 Da Aka Yi Garkuwa Da Su Bayan Kashe Ɗan Bindiga A Katsina
  • Al’ummar Karamar Hukumar Maigatari Sun Bukaci Gwamnatin Jigawa Ta Gina Musu Hanyoyi
  • Gwamnatin Kano Ta Fidda Sabbin Dokoki Domin Yaƙi Da Gurɓata Muhalli
  • Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Zamfara Ta Tabbatar Da Harin ‘Yan Bindiga A Banga
  • Zuba Jari Daga Kasashen Waje A Noman Zamani: Jigawa Ta Baje Kolin Aikin Noma A Abuja
  • Majalisar Jihar Kaduna Ta Bude Bincike Kan Ginin Kasuwa da Aka Yi Watsi da Shi
  • Gwamna Zulum Ya Yi Allah-wadai Da Sabbin Hare-haren Boko Haram Da Sace-sacen Mutane A Borno
  • Gwamnatin Kasar Aljeriya Ta Dakatar Da Zirga-Zirgan Jiragen Saman Kasar Zuwa Kasar Mali
  • Matsalar tsaro: Ba za mu lamunci zagon ƙasa ba — Gwamnatin Sakkwato
  • Harin Filato: An kashe Mutane 40, An Kona Gidaje 383, Fiye Da Mutane 1,000 An Raba Su Da Muhallansu