Shugaban karamar hukumar Arewa ta jihar Kebbi, Alhaji Sani Aliyu, ya tabbatar da harin da ‘yan ta’addan Lakurawa suka kai a yankin, inda suka kashe mutane kimanin 15 tare da kona kauyuka 7.

Da yake tabbatar da faruwar lamarin ga gidan rediyon Najeriya da ke jihar Kebbi, shugaban karamar hukumar ya ce an baza jami’an tsaro a yankin domin tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin al’umma.

A cewar wata majiya mai tushe, Malam Umar, maharan sun kara kona akalla wasu kauyuka bakwai da ke kusa da Birnin Dede, duk a cikin karamar hukumar Arewa ta jihar Kebbin.

A wata tattaunawa ta wayar tarho, Malam Umar ya bayyana cewa, an kai harin ne domin ramuwar gayya kan kisan da jami’an tsaro suka yi wa shugaban nasu a makon da ya gabata, inda ya kara da cewa, maharan sun bar kauye daya ne kawai, wanda sojoji ke gadinsa.

“Harin na daren Lahadin da ta gabata tamkar ramuwar gayya ne biyo bayan kashe shugaban Lakurawa, Maigemu da hadin gwiwar jami’an tsaro suka yi a Kebbi”. 

Sai dai Kakakin Rundunar ’Yan sandan Jihar Kebbi, SP Nafiu Abubakar, bai amsa kiran waya ko sakon waya da ake neman karin bayani kan lamarin ba.

 

Daga Abdullahi Tukur

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Lakurawa

এছাড়াও পড়ুন:

Alummomin duniya na ci gaba da yin Allah wadai da kisan fararen hula a Siriya

Majalisar Dinkin Duniya ta yi Allah wadai da tashin hankalin da ya farke a gabar tekun Syria a ranar Lahadin da ta gabata, a daidai lokacin da rahotanni ke nuna cewa an kashe wasu iyalai baki daya a wannan tashin hankali, abin da Majalisar Dinkin Duniya ta bayyana a matsayin “mai matukar tayar da hankali”.

Babban jami’in kare hakkin bil’adama na Majalisar Dinkin Duniya, Volker Turk, ya yi kira da a gaggauta gudanar da bincike kan kisan kiyashin da masu dauke da makamai suka aikata, tare da hukunta wadanda suka aikata laifukan.

Babban jami’in kare hakkin bil adama na MDD ya kara da cewa, “Muna samun rahotanni masu matukar tayar da hankali kan yadda ake kashe iyalai baki daya, da suka hada da mata da yara,  yana mai jaddada kira a kan dole ne a daina kashe fararen hula a yankunan gabar teku a arewa maso yammacin Syria.

Ya yi kira da a gudanar da bincike na gaskiya cikin gaggawa ba tare da nuna son kai ba, kan dukkan kashe-kashe da sauran cin zarafin da aka aikata, ya kara da cewa “wajibi ne a hukunta wadanda suka aikata hakan bisa ka’idoji da dokokin kasa da kasa.

A nasa bangaren, shugaban hukumar lafiya ta duniya ya bayyana fadan a matsayin abin damuwa sosai tare da tabbatar da cewa hakan yana yin mummunar  illa ga lafiyar mutane kai tsaye, domin kuwa a rusa cibiyoyin lafiya da motocin daukar marasa lafiya.

Tedros Adhanom ya wallafa cewa, “WHO tana aiki tukuru don isar da magunguna cikin gaggawa, don kulawa ta gaggawa ga wadanda suka jikkata.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tutocin Falasdinu Sun Yi Ta Kadawa A Birnin Sao Paulo Na kasar Brazil, A Gagarumin Gaggami Da Masu Goyon Bayan Falasdinawa Suka Shirya
  • Gwamnatin Kano Ta Bullo Da Sabbin Hanyoyin Kare Makarantunta Daga Kalubalen Tsaro
  • ‘Yan Sanda Sun Fara Bincike Kan Kisan Shugaban Kungiyar Miyetti Allah A Kwara
  • Alummomin duniya na ci gaba da yin Allah wadai da kisan fararen hula a Siriya
  • Shugaba Tinubu Ya Nada Jega Mai Ba Shi Shawara Na Musamman Kan Harkokin Kiwon Dabbobi
  • Hukumar Raya Arewa maso Yamma Ta Kai Ziyara Jihar Jigawa
  • Hajjin 2025: Ba Zan Taba Bai Wa Tinubu Da ‘Yan Nijeriya Kunya Ba – Shugaban NAHCON
  • An kashe shugaban Lakurawa, Maigemu a Kebbi
  • Rundunar Tsaro Ta Yi Nasarar Hallaka Wani Jigo Lakurawa A Kebbi