Masu rajin kare hakkin bil’adama a birnin Sao Paulo na kasar Brazil, sun ratsa tsakiyar birnin tare da makeken tutar kasar Falasdinu inda suke kira zuwa ga cikekken yenci ga Falasdinawa da kuma dakatar da kissan kiyashin da HKI take aikatawa a can.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa, a dai dai lokacinda ake kira zuwa ga goyin bayan mutanen gaza wadanda HKI takewa kissan kiyashi a fagen kasa da kasa, mutanen Brazil sun fito kwansu da kwarkwartansu a birnin Sao Paulo don tabbatar da wannan kiran.

A halin yanzu dai ana kokarin samarda kawance ta kasa da kasa, wacce zata game ko ina a duniya, don goyon bayan mutanen Falasdinu da kuma korar yahudawa yan mulkin mallaka kuma yan mamaya, daga kasar Falasdinu da aka mamaye.

Labarin ya kara da cewa, wadanda suka yi jawabi a gaggamin taron na Sao Paulo sun bukaci a kawo karshen kissan kiyashi a Gaza, a kuma kafa kasar Falasdinu mai cikekken yenci daga teku zuwa kogi.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Jiragen Yaki Da Sojojin Kasa Na HKI Sun Kashe Falasdinawa 38 A Yankin Gaza Daga Safiyar Yau Zuwa Yanzu

Jiragen yakin HKI sun kashe akalla mutane 38 a wurare daban-daban a zirin Gaza, kuma mafi yawan wadanda ta kashen yara kanana ne.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto majiyar Falasdinawa a Gaza na cewa da sassafe jiragen yakin sun kaiwa wani gidan Bene a unguwar shujaiyya na wajen garin Gaza inda a nan take suka kashe falasdinawa kimani 30 sannan wasu da dama suka ji rauni.

Sai kuma a kan sansanin yan gudun hijira na Nusairat jiragen yakin HKI sun kashe muatne akalla 8 wanda ya kawo jimillar wadanda aka kashe zuwa lokacin bada wannan labarin zuwa 38. Wasu da dama sun ji rauni. Raunukan wasu yana da hatsari mai yuwa yam utu nan gaba.

Sannan majiyar sojojin HKI ta bayyana cewa zuwa lokacin bada wannan labaran sun kai hare-hare har gusa 45 a kan yankuna daban daban a gaza.

Tun ranar 7 ga watan Octoban shekara ta 2023 dai zuwa yanzo sojojin yahudawan HKI sun kashe Falasdinawa akalla dubu 51.a yayinda wasu fiye da dubu 100 sun ji rauni.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mutanen da suka saba ba ni abinci yanzu na neman taimako — Obi
  • Jiragen Yaki Da Sojojin Kasa Na HKI Sun Kashe Falasdinawa 38 A Yankin Gaza Daga Safiyar Yau Zuwa Yanzu
  • Hamas Ta Yi Allawadai Da Gwamnatin Falasdinawa Kan Masu Goyon Bayanta A Yankin Yamma Da Kogin Jordan
  • Yan Sanda A Saudiya Sun Tsare Wata Bafalasdinya Saboda Bayyana Tutar Kasarta A Kan Jakarta A Masallacin Ka’aba
  • Sharhin Bayan Labarai: Zanga-Zanga A Kasashen Larabawa Ta Goyon Bayan Falasdinaw A Gaza
  • Ambaliyar ruwa ta kashe mutum 30 a Kongo
  • Matakin Sin Na Karfafa Takaita Fitar Da Abubuwa Masu Alaka Da Ma’adanan “Rare Rarth” Na Nuni Ga Aniyarta Ta Kare Tsaron Kasa
  • Ambaliya Ta Hallaka Mutum 30 A Birnin Kinshasa Na Jamhuriyar Demokradiyar Congo
  • Iran : kasashen turai sun tafka kure na tarihi, ta hanyar goyan bayan Isra’ila
  • Mutanen da Sanƙarau ta kashe sun kai 151 — NCDC