Gina Mutane Don Bunkasa Hazakarsu Na Daga Cikin Ajendar Sin Na 2025
Published: 10th, March 2025 GMT
Kirkira ita ce kashin bayan ci gaba, kuma hazaka ita ce ginshikin kirkira. A zamanin yau, fannoni masu tasowa musamman na fasahar zamani kamar kirkirarriyar basira (AI) da sauransu suna bunkasa, kuma akwai bukatu na matukar gaggawa ga sabbin hazaka. Hakan ya sanya kasar Sin ta maida hankali kan raya hazaka tun wuri-wuri, da kara zuba jari a fannin ilimi, da dasa iri na kirkire-kirkire don ya tsira a cikin zukatan matasa ta hanyar “zuba jari kan gina mutane”.
Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya halarci taron tattaunawa da nazari kan ganawar da wakilan jam’iyyar CPPCC daga fannonin kimiyya, fasaha da ilimi, wanda ya fitar da kwakkwaran matakai game da hangen nesa a ranar 6 ga watan nan da muke ciki, wanda ya jaddada muhimmancin kimiyya da fasaha da ilimi da hazaka ga zamanantar da kasar Sin, inda shugaba Xi ya jaddada cewa a nan gaba, ya kamata kasar Sin ta rungumi wani yanayi mai haske, inda za a samu masu kwazo da hazaka masu dimbin yawa, ta yadda kowa da kowa zai baje kolin basirarsa kuma a yi amfani da su yadda ya kamata. Har ila yau, a cikin rahoton aikin gwamnati na bana, an gabatar da sabbin dabarun “zuba jari kan gina mutane” a karon farko, wanda kamar fitila, ya haskaka muhimmin alkibla ga ci gaban kasar Sin a nan gaba. Sanin kowa ne cewa, a cikin ’yan shekarun nan, gwamnatin kasar Sin a dukkan matakai ta samu sakamako mai ban mamaki a fannonin zuba jari na zahiri wadanda suka shafi ababen more rayuwa, da kawo sabbin salon gudanar da harkokin birane da kauyuka. (Mohammed Yahaya)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Harin Lakurawa: An Kashe Mutane 15 Tare Da Kona Kauyuka 7 A Birnin Kebbi
Shugaban karamar hukumar Arewa ta jihar Kebbi, Alhaji Sani Aliyu, ya tabbatar da harin da ‘yan ta’addan Lakurawa suka kai a yankin, inda suka kashe mutane kimanin 15 tare da kona kauyuka 7.
Da yake tabbatar da faruwar lamarin ga gidan rediyon Najeriya da ke jihar Kebbi, shugaban karamar hukumar ya ce an baza jami’an tsaro a yankin domin tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin al’umma.
A cewar wata majiya mai tushe, Malam Umar, maharan sun kara kona akalla wasu kauyuka bakwai da ke kusa da Birnin Dede, duk a cikin karamar hukumar Arewa ta jihar Kebbin.
A wata tattaunawa ta wayar tarho, Malam Umar ya bayyana cewa, an kai harin ne domin ramuwar gayya kan kisan da jami’an tsaro suka yi wa shugaban nasu a makon da ya gabata, inda ya kara da cewa, maharan sun bar kauye daya ne kawai, wanda sojoji ke gadinsa.
“Harin na daren Lahadin da ta gabata tamkar ramuwar gayya ne biyo bayan kashe shugaban Lakurawa, Maigemu da hadin gwiwar jami’an tsaro suka yi a Kebbi”.
Sai dai Kakakin Rundunar ’Yan sandan Jihar Kebbi, SP Nafiu Abubakar, bai amsa kiran waya ko sakon waya da ake neman karin bayani kan lamarin ba.
Daga Abdullahi Tukur