Kirkira ita ce kashin bayan ci gaba, kuma hazaka ita ce ginshikin kirkira. A zamanin yau, fannoni masu tasowa musamman na fasahar zamani kamar kirkirarriyar basira (AI) da sauransu suna bunkasa, kuma akwai bukatu na matukar gaggawa ga sabbin hazaka. Hakan ya sanya kasar Sin ta maida hankali kan raya hazaka tun wuri-wuri, da kara zuba jari a fannin ilimi, da dasa iri na kirkire-kirkire don ya tsira a cikin zukatan matasa ta hanyar “zuba jari kan gina mutane”.

Matakan da aka ambata a cikin rahoton aikin gwamnati a taruka biyu na bana, kamar bayar da tallafin tarbiyyar yara da karfafa tsare-tsaren tabbatar da kowane yaro ya samu ilimi ala tilas, ayyuka ne masu haske ga wannan manufa ta “zuba jari kan gina mutane” a fagen ilimi. Wannan manufa ba wai kawai ta mayar da hankali kan daidaikun mutane ba ne, har ma da la’akari mai zurfi ga ci gaban al’umma gaba daya. Manufar tana kuma mayar da hankali ga dukkan tsarin rayuwa la’akari da yanayi mai sarkakiya da muke ciki. Hakazalika, tsarin daidaitawa da fadada ayyukan yi na ba da cikakkiyar damar nuna hazakar mutane da kuma fahimtar kimarsu, kamar dai yadda tsarin bunkasa yawan kudin shiga na mazauna ke iya habaka tunaninsu game da hanyoyin samun riba da karin farin ciki da kwanciyar hankali.

Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya halarci taron tattaunawa da nazari kan ganawar da wakilan jam’iyyar CPPCC daga fannonin kimiyya, fasaha da ilimi, wanda ya fitar da kwakkwaran matakai game da hangen nesa a ranar 6 ga watan nan da muke ciki, wanda ya jaddada muhimmancin kimiyya da fasaha da ilimi da hazaka ga zamanantar da kasar Sin, inda shugaba Xi ya jaddada cewa a nan gaba, ya kamata kasar Sin ta rungumi wani yanayi mai haske, inda za a samu masu kwazo da hazaka masu dimbin yawa, ta yadda kowa da kowa zai baje kolin basirarsa kuma a yi amfani da su yadda ya kamata. Har ila yau, a cikin rahoton aikin gwamnati na bana, an gabatar da sabbin dabarun “zuba jari kan gina mutane” a karon farko, wanda kamar fitila, ya haskaka muhimmin alkibla ga ci gaban kasar Sin a nan gaba. Sanin kowa ne cewa, a cikin ’yan shekarun nan, gwamnatin kasar Sin a dukkan matakai ta samu sakamako mai ban mamaki a fannonin zuba jari na zahiri wadanda suka shafi ababen more rayuwa, da kawo sabbin salon gudanar da harkokin birane da kauyuka. (Mohammed Yahaya)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Harin Lakurawa: An Kashe Mutane 15 Tare Da Kona Kauyuka 7 A Birnin Kebbi

Shugaban karamar hukumar Arewa ta jihar Kebbi, Alhaji Sani Aliyu, ya tabbatar da harin da ‘yan ta’addan Lakurawa suka kai a yankin, inda suka kashe mutane kimanin 15 tare da kona kauyuka 7.

Da yake tabbatar da faruwar lamarin ga gidan rediyon Najeriya da ke jihar Kebbi, shugaban karamar hukumar ya ce an baza jami’an tsaro a yankin domin tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin al’umma.

A cewar wata majiya mai tushe, Malam Umar, maharan sun kara kona akalla wasu kauyuka bakwai da ke kusa da Birnin Dede, duk a cikin karamar hukumar Arewa ta jihar Kebbin.

A wata tattaunawa ta wayar tarho, Malam Umar ya bayyana cewa, an kai harin ne domin ramuwar gayya kan kisan da jami’an tsaro suka yi wa shugaban nasu a makon da ya gabata, inda ya kara da cewa, maharan sun bar kauye daya ne kawai, wanda sojoji ke gadinsa.

“Harin na daren Lahadin da ta gabata tamkar ramuwar gayya ne biyo bayan kashe shugaban Lakurawa, Maigemu da hadin gwiwar jami’an tsaro suka yi a Kebbi”. 

Sai dai Kakakin Rundunar ’Yan sandan Jihar Kebbi, SP Nafiu Abubakar, bai amsa kiran waya ko sakon waya da ake neman karin bayani kan lamarin ba.

 

Daga Abdullahi Tukur

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji Sun Miƙawa Gwamnatin Borno Mutane 75 Da Suka Ceto
  • Harin Lakurawa: An Kashe Mutane 15 Tare Da Kona Kauyuka 7 A Birnin Kebbi
  • Sama da mutane 1,000 suka mutu a rikicin Siriya
  • Nazarin CGTN: Mutane Da Dama A Duniya Sun Yaba Da Salon Shugabancin Gwamnatin Kasar Sin 
  • Mutane 1,018 ne aka kashe a ci gaba da kisan kiyashi kan tsiraru a gabar tekun Syria
  • Ta’addancin yankin Sahel ya ninka na sauran sassan duniya — Rahoto
  • Jamus, Faransa, Birtaniya Da Italiya Sun Yi Maraba Da Shirin Larabawa Kan Gaza
  • Girke-girkenmu Na Azumi
  • Abubuwan Sha Domin Karin Ni’ima Ga Mata