Abba zai naɗa sabon Kwamishina a Kano
Published: 10th, March 2025 GMT
Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf ya miƙa wa majalisar dokokin jihar sunan Ibrahim Yakubu Adamu domin tantancewa da tabbatar da naɗinsa a matsayin sabon Kwamishina.
Kakakin Majalisar, Alhaji Jibrin Falgore ne ya bayyana hakan yayin da yake karanta wasiƙar gwamnan a zaman majalisar da ya gudana a yau Litinin.
Aminiya ta ruwaito cewa, Ibrahim Yakubu Adamu wanda gwamnan ke shirin naɗawa muƙamin kwamishina shi ne Shugaban Hukumar Tsara Birane ta Kano, KNUPDA.
Falgore ya ce nan gaba kaɗan za su aika masa goron gayyata domin tabbatar da buƙatar gwamnan.
Kazalika, majalisar ta kuma tabbatar da dokar kafa sabuwar Hukumar Kula da Gine-Ginen Gwamnati da Ababen More Rayuwa.
Shugaban masu rinjaye na majalisar, Lawan Hussein na jam’iyyar NNPP daga Ƙaramar Hukumar Dala, ya ce sabuwar hukumar ce za ta riƙa ɗawainiyar kula da gine-ginen gwamnati da sauran ababen more rayuwa da suka haɗa da tituna, gadoji da sauransu.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ibrahim Yakubu Adamu Jihar Kano
এছাড়াও পড়ুন:
Dalilin da muka dakatar da Sanata Natasha — Majalisar Dattawa
Majaliar Dattawa ta ce ta dakatar da Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan ne saboda saɓa dokokin majalisar da ta yi, ba don zargin cin zarafin da ta yi wa shugaban majalisar ba.
Shugaban masu rinjaye na majalisar, Sanata Bamidele Opeyemi ne bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Asabar a madadin majalisar.
Kotu ta saki tsohon shugaban Koriya ta Kudu, Yoon Suk Yeol Ramadan: Hisbah ta rufe shagon caca a KanoA cewarsa, dakatar da Sanata Natasha, mataki ne da duka majalisar ta ɗauka, saboda saɓa dokokinta da ta yi kamar yadda kwamitin ɗa’a da ladabtarwa ya tabbatar.
“An dakatar da ita ne saboda yadda take keta dokoki da ƙa’dojin majalisa, da nuna rashin ɗa’a a majalisar, wannan shi ne laifinta babu daɗi babu ragi.”
Sanarwar ta ce da a ce Sanata Natasha ta yi aiki da dokoki da ƙa’idojin majalisar, da majalisar za ta karɓi ƙorafinta, kamar yadda doka ta tanada.
“Amma ba ta bi ƙa’ida da dokokin da suka kafa majalisar da take aiki a cikinta ba.”
Sanata Bamidele ya ce majalisar ta ɗauki matakin dakatar da Sanata Natasha ne bisa shawarar kwamitin ɗa’a, wanda ya same ta da laifin saɓa wa sashe na 6.1 da sashe na 6.2 na dokokin majalisar.
Sanarwar ta kuma zayyano wasu laifuka biyar da ta ce Sanata Natasha ta aikata, ciki har da ƙin zama a kujerar da aka sauya mata a lokacin zaman majalisar na ranar 25 ga watan Fabrairu, da yin magana ba tare da amincewar jagoran zaman majalisar ba, da yin kalaman zagi da rashin girmamawa da shugabancin majalisar.
Aminiya ta ruwaito cewa, a ranar Alhamis da ta gabata ce Majalisar Dattawan Najeriya ta dakatar da Sanata mai wakiltar Kogi ta Tsakiya, Sanata Natasha Akpoti Uduaghan har na tsawon wattani shida a kan laifin saɓa wa dokokin majalisar.