Sojoji Sun Miƙawa Gwamnatin Borno Mutane 75 Da Suka Ceto
Published: 10th, March 2025 GMT
Da yake jawabi a wurin taron, Maj.-Gen. Waidi Shuaibu, kwamandan OPHK, ya ce matakin na daga cikin kokarin da ake yi na tabbatar da zaman lafiya a yankin da kuma dawo da wadanda rikicin Boko Haram ya shafa.
Shuaibu ya jaddada aniyar rundunar na dawo da zaman lafiya a yankin Arewa maso Gabas ta hanyar kawar da barazanar masu tada kayar baya.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Bai wa ’yan bindiga kuɗin fansa na dagula sha’anin tsaro — Ribadu
Mai Bai Wa Shugaban Ƙasa Shawara kan Sha’anin Tsaro, Nuhu Ribadu, ya roƙi ’yan Najeriya da su daina biyan ’yan bindiga da masu garkuwa da mutane kuɗin fansa.
Ribadu, ya ce biyan kuɗin fansa ba ya sa ana sakin waɗanda aka sace, kuma hakan na ƙara dagula al’amuran tsaro.
Harajin China da Amurka: Mece ce makomar tattalin arziƙin duniya? Za a ci gaba da sayar da ɗanyen mai a farashin Naira — GwamnatiRibadu ya bayyana haka ne a ranar Talata a Abuja, yayin da yake karɓar mutane 64 da dakarun tsaro suka ceto daga hannun masu garkuwa da su a Zangon Kataf da ke Kudancin Kaduna.
“Don Allah ku daina bai wa waɗannan mutane (masu garkuwa) kuɗi, wannan shi ne babban ƙalubalen da muke fuskanta,” in ji Ribadu.
“Da yawa daga cikin iyalan waɗannan mutanen sun riga sun biya kuɗin fansa, amma hakan bai sa an sako su ba. Mu ne jami’an tsaro muka kuɓutar da su.”
Ya ƙara da cewa: “Ba kuɗin da ake ba su ne ke kawo sakamakon da ake so ba.
“Waɗannan mutanen, duk lokacin da kuka ba su kuɗi, sai su ƙara inganta aikinsu.
“Ba mu taɓa bai wa kowa ko sisin kwabo ba, kuma ba ma son mutane su ci gaba da yin hakan.”
Ribadu, ya ce ci gaban da aka samu wajen ceto waɗanda aka sace ya samu ne sakamakon jajircewar dakarun soji da sauran hukumomin tsaro.
“Ina matuƙar yaba wa dakarunmu da hukumomin tsaro. Jajircewarsu wajen bin diddigin waɗannan miyagu shi ne dalilin da ya sa muke a nan yau,” in ji Ribadu.
“Saboda jajircewar Shugaban Ƙasa, kullum muna samun ci gaba. Amma sako waɗanda aka kama ba shi ne ƙarshen wannan abu ba.
“Za mu ci gaba da bin diddigin waɗannan ’yan ta’adda har sai sun fuskanci hukunci.”
Mutum 64 da aka ceto sun kwashe sama da wata guda a hannun waɗanda suka sace su.
Daga cikinsu akwai mataimakin darakta a ma’aikatar gwamnati da kuma wani ɗan uwan Bishop Matthew Hassan Kukah na cocin Katolika da ke Jihar Sakkwato.