’Yan bindiga sun kashe manoma 14 a Ondo
Published: 11th, March 2025 GMT
’Yan bindiga sun kashe aƙalla manoma 14 yayin wani hari da suka kai yankuna huɗu a Ƙaramar Hukumar Akure ta Arewa da ke Jihar Ondo.
Yankunan da abin ya shafa — Aba Alajido, Aba Sunday, Aba Pastor da Ademekun— galibi mazaunansu ƙananan manoma ne.
Abba zai naɗa sabon Kwamishina a Kano Yadda za a samu rufin asiri da sana’ar ɗinki — MuhammadWata majiyar ’yan sanda, ta tabbatar da faruwar lamarin, tana mai cewa maharan ɗauke da bindigogi sun auka yankunan ne da tsakar daren ranar Asabar inda suka soma harbe-harbe kan mai uwa da wabi.
Majiyar ta ce kawo yanzu dai an tsinto gawawwaki mutum 14 yayin da ake ci gaba laluben wasu.
Wani mazaunin ɗaya daga cikin yankunan da abin ya shafa da ya buƙaci a sakaya sunansa, ya ce har kawo yanzu wasu daga mutanensu da suka tsere cikin jeji ba su dawo ba.
Ya ce tun a ranar Litinin ta makon jiya aka soma kawo musu hari, sai dai mafi munin ciki shi ne wanda ya auku a ranar Juma’a ba tare da maharan sun fuskanci wata tirjiya ba.
“Tun cikin daren ranar Juma’a suka soma kawo mana kuma duk wanda suka gani sai su buɗe masa wuta.
“Mutanenmu da dama sun gudu neman mafaka a jeji kuma ina tsammanin zuwa yanzu sun kashe mutum fiye da 40 a ƙauyukan yayin da wasu da dama sun jikkata.”
Da take zantawa da Aminiya ta wayar tarho, mai magana da yawun rundunar ’yan sandan jihar, Funmilayo Odunlami-Omisamya, ta tabbatar da faruwar lamarin.
A cewarta, an soma gudanar da bincike kan lamarin wanda kawo yanzu an tsinto gawawwakin mutum 14 a jeji.
Ta ce an tura tawagar jami’an ’yan sanda da za ta bi sawun ɓata-garin kuma tuni tarzoma ta lafa a yankin.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindiga jihar Ondo
এছাড়াও পড়ুন:
Abin da ya sa na sauya sheƙa daga APC zuwa SDP — El-Rufai
Tsohon Gwamnan Kaduna, Nasir El-Rufa’i ya tabbatar da sauya sheƙa daga jam’iyyar APC mai mulkin ƙasar zuwa jam’iyyar SDP.
Hakan na ƙunshe cikin wata sanarwa da ya wallafa ranar Litinin ne a shafukansa na sada zumunta.
’Yan bindiga sun yi garkuwa da matashi a Kano Tsohon Mataimakin Gwamnan Kogi Patrick Adaba ya rasuEl-Rufai ya ce, “yanzu na yanke shawarar komawa jam’iyyar Social Democratic Party, kuma zan kasance a cikin ta wajen tafiyar da al’amurana na siyasa a nan gaba.
Ya ce a matsayinsa na wanda aka kafa jam’iyyar APC da shi, zai ci gaba da tunawa da faɗi tashi da kuma kyakkyawar mu’amalar da ya yi da duk abokan hulɗarsa.
Ya ce ya yi fatan cewa jam’iyyar APC wadda da shi aka kafa ta tun a shekarar 2013 za ta tsaya a kan tubalin da suka assasa ta har zuwa lokacin da zai yi ritaya daga siyasa.
Sai dai ya ce a tsawon shekaru biyu da suka gabata, ya lura cewa akwai halin ko-in-kula gami da sauka daga kan tsari da aƙida a ɓangaren waɗanda ke riƙe da madafan ikon jam’iyyar a yanzu, da ba su da burin magance matsalolin da suka addabi jam’iyyar.
Ya ce a nasa ɓangaren, ya bayyana damuwa a cikin sirri da kuma kwanan a bainar jama’a game da halin da jam’iyyar take ciki, amma ya ga babu mafita face ficewa daga jam’iyyar domin sauya sheƙa zuwa wata da zai ci gaba da gudanar da al’amuran siyasa da zai kawo ci gaba a Jihar Kaduna, Arewa da kuma Nijeriya baki ɗaya.
“A matsayina na ɗan jam’iyya mai kishi, na yi aiki wajen taimaka wa jam’iyyar APC ta samun nasara a zaɓukan 2015, 2019 da 2023.
“Ina ɗaya daga cikin gwamnoni da dama da aka zaɓa a ƙarƙashin inuwar jam’iyyar a 2015 da 2019, waɗanda suka tsaya tsayin daka wajen tabbatar da dimokuradiyya da ka’idojin ciyar da ƙasa gaba.
“Tsawon shekaru takwas da na yi a matsayin Gwamnan Jihar Kaduna, na duƙufa wajen aiwatar da tsare-tsare masu inganci don ciyar da al’umma gaba a fannin ilimi da kiwon lafiya, da faɗaɗa ababen more rayuwa, samar da ayyukan yi da jawo jari.
“Waɗannan bayanan kaɗan ne a cikin manufofin da jam’iyyar APC mai ci ta yi watsi da su a yanzu tare da wulaƙanta mambobinta a shekaru biyu da suka gabata. Na ga abin ba mai karɓuwa ba ne.
“A yau 10 ga Maris, 2025, na miƙa takardar barin jam’iyyar APC a mazaɓata ta Kaduna.
“Sai dai kafin ɗaukar wannan matakin, na kammala tuntuɓar mashawarta, abokan aiki da magoya baya a duk faɗin ƙasar game da hakan.
“A yanzu na yanke shawarar shiga jam’iyyar Social Democratic Party (SDP), kuma na ɗauke ta a matsayin inuwar gudanar da harkokina na siyasa da sauran ayyuka.
“Saboda haka, zan mayar da hankali wajen yin cuɗanya tare da jawo hankalin sauran ’yan jam’iyyun adawa su shigo cikinmu, mu taru a karkashin tsarin dimokuraɗiyya bai ɗaya domin ƙalubalantar jam’iyyar APC a duk wani zaɓe da zaɓen fidda gwani da za a yi daga yanzu zuwa 2027 da yardar Allah.
“Don haka ina kira ga dukkan magoya bayanmu da sauran waɗanda suka damu da makomar ƙasarmu da su shigo jam’iyyar SDP don ganin Nijeriya ta bunƙasa a matsayin abin alfahari ga ‘yan Afirka da duk wani baƙar fata.”
Ana iya tuna cewa tun a kwanakin baya yayin tattaunawarsa da gidan talabijin na Arise, El-Rufa’i ya bayyana cewa “jam’iyyar APC ta sauka daga kan manufofin da aka assasa ta tun fil-azal.”
Ya yi zargin cewa jam’iyyar ta gaza kiran taron shugabanninta na ƙasa tsawon shekaru, wanda ya ce hakan ya saɓa wa tanade-tanaden kundin tsarin mulkin jam’iyyar.
A yanzu dai wannan ya kawo ƙarshen raɗe-raɗin da ake yi na inda tsohon gwamnan zai nufa bayan raba gari da jam’iyyar APC.