Leadership News Hausa:
2025-04-10@03:49:23 GMT

Tambuwal Ya Tallafawa Magidanta Dubu 30 Da Kayan Abinci

Published: 11th, March 2025 GMT

Tambuwal Ya Tallafawa Magidanta Dubu 30 Da Kayan Abinci

Tsohon gwamnan jihar Sakkwato, Sanata Aminu Waziri Tambuwal ya kaddamar da tallafin kayan abinci ga magidanta dubu 30 a fadin jihar.

A yayin da yake kaddamar da tallafin tare da bayar da jari ga masu kananan sana’oi a gidansa a ranar Litinin, ya bayyana cewar tallafin wani mataki ne na saukakawa mabukata halin kunci a watan Ramadan mai girma.

Sojoji Sun Miƙawa Gwamnatin Borno Mutane 75 Da Suka Ceto Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Alhinin Rasuwar Fitaccen Masanin Aikin Jarida, Kabir Ɗangogo

Tambuwal wanda ke wakiltar Sakkwato ta Kudu a majalisar dattawa, ya bukaci wadanda za su rarraba kayan abincin da su gudanar da gaskiya da adalci wajen tabbatar da tallafin ya kai hannun wadanda suka cancanta a mazabu 244 da yake wakilta.

Tambuwal ya kuma yabawa ‘yan majalisar dokoki na jiha da na tarayya da ke karkashin jam’iyyar PDP kan kokarin da suke yi wajen sauke nauyin al’umma da ke kan su a bisa ga kudurori da manufofin jam’iyyar PDP.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Zuba Jari Daga Kasashen Waje A Noman Zamani: Jigawa Ta Baje Kolin Aikin Noma A Abuja

A ci gaba da kokarinsa na kawo sabon tsari domin inganta harkokin noma a jihar Jigawa, Gwamna Malam Umar Namadi ya jagoranci tawagar gwamnatin jihar zuwa wani babban taro da manyan masu zuba jari na duniya da masu ruwa da tsaki a harkar noma. Taron wanda ya gudana jiya Talata a otal din Hilton da ke Abuja, ya kunshi wakilai daga kamfanonin SINOMACH, China CAMC Engineering Company Ltd, YTO Group Corporation, da Agra Consortium Ltd, da kuma asusun bunkasa noma na gwamnatin tarayya (NADFUND). Kyautar LEADERSHIP Ta Kara Zaburar Da Mu Kan Sauke Nauyin Al’ummar Jigawa Akanmu – Gwamna Namadi Kasar Sin Na Yaki Da Cin Zalin Da Amurka Ke Yi Ta Hanyar Dora Haraji Ne Bisa Sanin Ya Kamata Taron ya samar wa Gwamnatin Jihar Jigawa wani dandali na baje kolin kayayyakin gona da jihar ta yi fice akansu ga masu saka hannun jari, wanda ya bayyana tsare-tsaren kawo sauyi da nufin mayar da Jihar Jigawa a matsayin babbar cibiyar kasuwancin kayayyakin gona da bunkasa masana’antu a Nijeriya. Jihar na fatan samun hannun jari a bangaren Kamfanin hada takin zamani domin inganta harkar noma, kamfanin harhada Motocin noma na YTO, aiwatar da aikin noman rani a fadin hekta 600 da ke Hadejia, kamfanin Integrated Halal Products Hub, Mayankar dabbobi ta zamani mai karfin yanka dabbobi 2,500 a kullum da dai sauransu. Tunda farko, a nasa jawabin, Gwamna Namadi ya yi maraba da tawagogin manyan kamfanoni da suka zo don halartar taron baje kolin kayan gona na jihar Jigawa a babban birnin tarayya Abuja. Gwamna Namadi ya jaddada amfanin noma na Jigawa, inda ya ce kashi 80 cikin 100 na kadada miliyan 2.47 na jihar gonaki ne na noma, wanda ya hada da ruwa 242 da kuma Kasuwar Dabbobi ta Maigatari, wacce babu sama da ita a Afirka.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hajjin 2025: Jihar Kaduna Ta Yi Tanadin Masauki Na Musamman Ga Alhazan Bana
  • Mutanen da suka saba ba ni abinci yanzu na neman taimako — Obi
  • Zuba Jari Daga Kasashen Waje A Noman Zamani: Jigawa Ta Baje Kolin Aikin Noma A Abuja
  • Hadin Gwiwar Fasaha Tsakanin Sin Da Afrika Za Ta Inganta Tsarin Samar Da Abinci A Nahiyar Afrika
  • Majalisar Jihar Kaduna Ta Bude Bincike Kan Ginin Kasuwa da Aka Yi Watsi da Shi
  • Likitocin Nijeriya dubu 16 sun yi ƙaura zuwa ƙetare — Ministan Lafiya
  • Hukumar Alhazai Ta Jihar Jigawa Ta Ci Gaba Da Gudanar Da Taron Bita Ga Alhazai
  • Jam’iyyar Labour Ta Yi Barazanar Dakatar Da Peter Obi Da Gwamna Otti
  • Harin Filato: An kashe Mutane 40, An Kona Gidaje 383, Fiye Da Mutane 1,000 An Raba Su Da Muhallansu 
  • An sayar da kare mafi tsada a duniya