Tambuwal Ya Tallafawa Magidanta Dubu 30 Da Kayan Abinci
Published: 11th, March 2025 GMT
Tsohon gwamnan jihar Sakkwato, Sanata Aminu Waziri Tambuwal ya kaddamar da tallafin kayan abinci ga magidanta dubu 30 a fadin jihar.
A yayin da yake kaddamar da tallafin tare da bayar da jari ga masu kananan sana’oi a gidansa a ranar Litinin, ya bayyana cewar tallafin wani mataki ne na saukakawa mabukata halin kunci a watan Ramadan mai girma.
Tambuwal wanda ke wakiltar Sakkwato ta Kudu a majalisar dattawa, ya bukaci wadanda za su rarraba kayan abincin da su gudanar da gaskiya da adalci wajen tabbatar da tallafin ya kai hannun wadanda suka cancanta a mazabu 244 da yake wakilta.
Tambuwal ya kuma yabawa ‘yan majalisar dokoki na jiha da na tarayya da ke karkashin jam’iyyar PDP kan kokarin da suke yi wajen sauke nauyin al’umma da ke kan su a bisa ga kudurori da manufofin jam’iyyar PDP.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Ɗan Uwan Gwamnan Kano Da Malaman NNPP Sun Koma APC
Haka nan, wasu manyan jiga-jigan NNPP daga ƙaramar hukumar Gwale, Mahmoud Salisu Gwale da Farouk Ahmed Gwale, su ma sun koma APC.
Sanata Barau ya tabbatarwa da al’ummar Nijeriya cewa kofa a buɗe take ga kowa.
“A matsayina na Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, ina yi wa kowa hidima. Ko da kai ɗan PDP ne, LP, Kwankwasiyya, ko wata jam’iyya, ina tare da kai. Idan kana son shigowa APC, jam’iyyar jama’a, muna maraba da kai. Ƙara yawa, ƙara daɗi!” in ji shi.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp