Kasar Sin Ta Mayar Da Martani Kan Kalaman Sakataren Baitul Malin Amurka
Published: 11th, March 2025 GMT
Sakataren baitul malin Amurka Scott Bessent ya sha nanata cewa, tattalin arzikin kasar Sin ya dogara a kan kayayyakin da ake fitarwa zuwa kasashen ketare fiye da kima, kuma Amurka na neman yin ciniki bisa adalci da daidaito. Sai dai kuma, da yake mayar da martani a yau Litinin 10 ga watan Maris, yayin wani taron manema labaru na yau da kullum, mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin, Mao Ning ta yi nuni da cewa, maganar da ake yi a kullum kan “rasa madafa” da neman cikakken daidaiton cinikayya ta saba wa ilimin tattalin arziki na asali, da yin watsi da hukunci da muradun kamfanoni da masu sayayya na Amurka.
Mao Ning ta ce, halin da ake ciki na cinikayya a tsakanin Amurka da kasar Sin yanzu haka ya samo asali ne sakamakon rawar da kasuwanni ke takawa, kuma abubuwa da dama sun shafi tsarin tattalin arzikin kasashen biyu,da manufofin ciniki da kuma matsayin dalar Amurka.
Ta kara da cewa, kasar Sin ba ta taba neman cin bulus da gangan ba. Hasali ma, Amurka ce ta fi tsintar dami a kala daga cinikayyarta da Sin. Mao Ning ta jaddada cewa, ba a sauya wa tuwo suna, domin ko ta yaya Amurka ta sauya akalar abin, ba za ta iya boye yunkurinta na siyasantarwa da mayar da batutuwan tattalin arziki da cinikayya a matsayin makamin dakilewa da neman murkushe kasar Sin ba. (Abdulrazaq Yahuza Jere)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Harajin China da Amurka: Mece ce makomar tattalin arziƙin duniya?
Sabon rikici ya sake kunno kai tsakanin ƙasashen China da Amurka, yayin da shugaba Donald Trump, ya ƙara wa kayayyakin da ake shiga da su ƙasar daga China haraji zuwa kashi 104.
Wannan matakin ya shafi kayayyaki kamar wayoyin hannu, batir, kayan wasan yara da na’urorin wasanni.
Za a ci gaba da sayar da ɗanyen mai a farashin Naira — Gwamnati Likitocin Nijeriya dubu 16 sun yi ƙaura zuwa ƙetare — Ministan Lafiya China ta ce ba za ta zuba ido baChina ta bayyana cewa ba za ta zuba ido ta yi tagumi yayin da ake gallaza mata.
China ta mayar da martani da nata harajin kashi wanda ta ƙada zuwa kashi 34 kan kayayyakin Amurka, inda ta kuma ce tana shirin ƙara wani harajin.
Ta rage darajar kuɗinta (Yuan) domin ƙarfafa fitar da kayayyaki zuwa ƙasashen waje.
A lokaci guda kuma, ta fara bincike kan wasu manyan kamfanonin Amurka kamar Google, inda kuma ta ke shirin daƙile wasu muhimman albarkatu.
Masana tattalin arziƙi na gargaɗin cewa wannan rikici zai shafi ƙasashe da dama, musamman na nahiyar Asiya kamar Vietnam da Cambodia, waɗanda harajin zai shafa daga Amurka.
Ana kuma ganin cewa wannan zai iya janyo hauhawar farashin kayayyaki a Amurka da kuma raguwar sayayya daga China.
Wannan ba rikicin haraji ba ne – ƘwararruWasu ƙwararru sun bayyana cewa wannan ba kawai rikicin haraji ba ne, wata gwagwarmaya ce ta nuna iko a harkokin kasuwancin duniya.
Ko da yake tattalin arziƙin China na fuskantar tangarɗa a yanzu, amma masana na ganin tana iya ɗorewa, domin kauce wa nuna rauni ga matakin da Amurka ke kai mata.
A gefe guda kuwa, Amurka na fama da matsin lamba daga ‘yan kasuwa da masu zuba jari da ke jin tsoron sakamakon wannan rikici.
Masana na fargabar lokacin da rikicin zai ƙareMasana sun bayyana cewa da wuya a san yadda wannan rikici zai ƙare.
Amma ana fatan cewa shugabannin ƙasashen biyu za su zauna tattaunawa domin samun mafita.
Ƙasashen duniya na fargabar cewa idan ba a daidaita ba, rikicin na iya taɓa tattalin arzikin duniya gaba ɗaya.