NAJERIYA A YAU: Abubuwan Da ke Shirin Faruwa A Fagen Siyasar Najeriya
Published: 11th, March 2025 GMT
More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba
Fagen siyasar Najeriya na ci gaba da ɗaukar salo iri-iri yayin da ’yan kasa da dama suka yi kasaƙe suna jiran girgiza ta gaba wadda wasu suke ganin tsohon Gwamnan Jihar Kaduna Malam Nasir El-Rufai, ya ɗiga mata ɗanba.
A baya-bayan nan dai an yi ta tsegunguma da rade-radi a kana bin da wasu jiga-jigan ’yan siyasar ƙasar nan, musamman ’yan adawa da ’ya’yan jam’iyya mai mulki waɗanda suke takun saƙa da Shugaba Bola Ahmed Tinubu suke ƙullawa
Yanzu ta fara wari, an ji Malam Nasiru ya bayar da sanarwar ficewarsa daga jam’iyyar APC da tsallakawa zuwa SDP.
Shin ko me zai biyo bayan wannan girgiza da tsallen baɗaken Malam Nasiru da dirarsa suka haifar?
Wannan ne batun da shirin Najeriya a Yau na wannan lokaci zai duba.
Domin sauke shirin, latsa nan
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Siyasar Nijeriya Zaɓen 2027
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Da Armenia Suna Fara Atisayen Hadin Giwa Don Karfafa Tsaron Kan Iyakar Kasashen Biyu
Sojojin kasa na kasashen Iran ta Armenia sun fara atisayen soje na hadin guiwa a tsakaninsu, don kyautata tsaro na kan iyakar kasashen biyu na kuma tsawon kwanaki biyu.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa dakarun kare juyin juya halin musulunci na kasar Iran ne suke jagorantar wannan atisayen. Da nufin hana fasa korin muggan kwayoyi da kuma sulalewar yan ta’adda suka kan iyakokin kasashen biyu.
Burgediya Janar Sayyid Mortaza Mira’in babban hafsan sojojin kasa na IRGC ya bayyana cewa, wannan atisayennn yana nuna irin yadda sojojin IRGC suke da shirin kare kasar daggga duk wata barazana. Da kuma abota da kyautata makobtaka da kasashe mmmakobta.
Labarin ya kara da cewa ana gudanar da rawan dajin ne a kan kan iyakar kasashen biyu na nordooz.