Shugaban kasar Ghana, John Darmani Mahama ya nemi kungiyar Ecowas da ta amince da kungiyar kawancen kasashen Sahel din nan guda uku da suka balle daga cikinta.

Mista Mahama, ya bayyana hakan a kafofin sada zumunta a ranar Litini jim kadan gabanin ya ziyarci kasar Burkina faso, bayan ya kai irin wanan ziyara kasashen Mali da Nijar.

Ci gaba da huldar tattalin arziki da kasashen Mali, Nijar da Burkina Faso, na daga cikin jigon rangadin da shugaban Ghana ya kai a kasashen na AES.

Bayan birnin Bamako a ranar Asabar, shugaban kasar Ghana John Dramani Mahama ya je birnin Yamai a ranar Lahadi, inda wasu rahotanni ke cewa ya je ne da nufin dinke barakar da ke tsakanin kungiyar ta raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afirka (ECOWAS) da kasashen uku na Sahel.

Saidai a cikin wata sanarwa da aka karanta a gidan talabijin na Nijar, hukumomin kasar sun tabbatar da cewa kasashen sun tabbatar da aniyarsu ta karfafa dangantakar abokantaka da hadin gwiwa a tsakanin kasashensu a fannonin siyasa, tattalin arziki da tsaro.

Kafin Nijar, John Dramani Mahama ya je Mali inda Janar Assimi Goïta ya tarbe shi. A cewar fadar shugaban kasar Ghana, ganawar da aka yi tsakanin mutanen biyu ta ba da damar fara tattaunawa kan karfafa hadin gwiwa a fannin tsaro.

Shugaban na Ghana ya kuma yi amfani da wannan dama wajen bayyana mahimmancin kasuwanci ta hanyar tashoshin jiragen ruwa na Ghana da ke Tekun Atlantika ga Mali.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Ta’addancin yankin Sahel ya ninka na sauran sassan duniya — Rahoto

A karon farko alkaluman ta’addaci a yankin Sahel da ke nahiyar Afirka ya zarce na jimillar sauran sassan duniya, a cewar rahoton cibiyar GTI mai bincike kan ta’addanci a matakin duniya.

Rahoton ya nuna yawan kashe-kashe masu alaka da ta’addanci a Sahel, “ya zarce rabin jimillar adadin a duniya.”

Kotu ta saki tsohon shugaban Koriya ta Kudu, Yoon Suk Yeol Ramadan: Hisbah ta rufe shagon caca a Kano

Alkaluman sun nuna an kashe mutane 3,885 a yankin daga cikin mutane 7,555 da aka kashe a fadin duniya a dalilin ta’addanci.

Rahoto ya kara da cewa a yayin da adadin a matakin duniya ya ragu daga kimanin 11,000 a shekarar 2015, lamarin ya ninku sau 10 a yankin daga shekarar 2019, sakamakon yadda kungiyoyin ta’addaci ke fadada ayyukansu a yankin.

Ya ci gaba da cewa, yayin da ake samun daidaikum masu aikata ta’addanci a kasashen Yammacin Duniya, a yankin Sahel kuma ana samu karuwar kungiyoyi ta’addanci masu mubaya’a ga kungiyar IS da Alka’ida, irin su ISWAP da Boko Haram da sauransu.

Shugaban Cibiyar Binciken Tsaro ta Afirka, Niagalé Bagayoko, ya ce wadannan kuniyoyi, “suna kafa dokoki, a wani lokaci ma har gasa suke yi da juna wajen nuna iko.”

Cibiyar Nazarin Tattalin Arziki da Zaman Lafiya, mai bincike kan zaman lafiya da tashe-tashen hankula a duniya ce ta walla fa rahoton, wanda ya bayyana ta’addanci a matsyain “abin da kungiyoyin da ba gwamnati ba ke yi na barazana ko tursasawa ko tashin hankali domin cim-ma manufar siyasa ko tattalin arziki ko addini da sauransu.”

Yankin Sahel da rahoton ya ayyana dai ya kunshi kasashe 10 — Burkina Faso, Mali, Nijar, Kamaru, Guinea, The Gambia, Senegal, Nijeriya, Chadi da uma Mauritania — kuma a nan ne sulusin mutane ’yan kasa da shekara 25 a fadin duniya suke.

GTI ta bayyana cewa tun bayan juyin mulkin kasar Mali a shekarar 2020 da 201 kungiyar IS-Sahel take ta fadada ikonta a iyakar kasar da Burkina Faso da Nijar, haka ma kungiyar JNIM, inda suke ta daukar karin mayaka, ciki har da kananan yara.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sharhin Dangane da: Atisayen Damarar Tsaro Ta 2025 Tsakanin Kasashen China, Rasha Da Iran
  •  Uganda Ta Aike Da Sojoji Zuwa Sudan Ta Kudun Domin Kare Babban Birnin Kasar
  • Harin Lakurawa: An Kashe Mutane 15 Tare Da Kona Kauyuka 7 A Birnin Kebbi
  • ‘Yan Sanda Sun Fara Bincike Kan Kisan Shugaban Kungiyar Miyetti Allah A Kwara
  • Shugaban Ghana ya ziyarci kasashen Sahel da suka balle daga Ecowas
  • Sharhin Bayan Labarai: Kasashen Afirka Sun Kori Sojojin Faransa Daga Kasashensu
  • A Gobe Litinin Za A Yi Atisayen Sojan Ruwa Na Hadin Gwiwa Tsakanin Kasashen Iran, Rasha Da China
  • An harbe shugaban ƙungiyar Miyetti Allah a Kwara
  • Ta’addancin yankin Sahel ya ninka na sauran sassan duniya — Rahoto