HausaTv:
2025-04-12@07:07:16 GMT

Zelensky ya je Saudiyya domin tattaunawar zaman lafiya

Published: 11th, March 2025 GMT

Shugaban kasar Ukraine Volodymyr Zelenskyy ya isa kasar Saudiyya domin ganawa da yarima mai jiran gado Mohammed bin Salman, gabanin wata muhimmiyar ganawa tsakanin tawagogin Ukraine da na Amurka domin share fagen shawarwarin zaman lafiya da Rasha a nan gaba.

Taron dai na nuni da wani gagarumin yunkurin diflomasiyya na magance rikicin da ke faruwa a Ukraine kuma zai iya ba da damar tsagaita bude wuta a cewar rahotanni.

Tattaunawar da za a yi a Jeddah ita ce ganawa ta farko tsakanin jami’an Ukraine da Amurka tun bayan ziyarar da Zelensky ya kai fadar White House a karshen watan Fabrairu da ya gabata, wanda ya haifar da cacar baki baki mai zafi tsakaninsa da shugaban Amurka Donald Trump.

Tun bayan hakan ne, gwamnatin Washington ta dakatar da taimakon soji ga Ukraine, lamarin da ya sa Kyiv ta nemi sulhu.

Zelenskyy ya bayyana cewa, “Muna fatan tattaunawa tare da amincewa kan shawarwari da ayyukan da suka dace,” yana mai jaddada cewa Ukraine na goyon bayan tattaunawa mai ma’ana tare da son a yi la’akari da muradunta.

Taron na ranar Talata zai mayar da hankali ne kan kafa tsarin zaman lafiya da tsagaita bude wuta tsakanin Rasha da Ukraine.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisar Jihar Kaduna Ta Bude Bincike Kan Ginin Kasuwa da Aka Yi Watsi da Shi

 

Majalisar Dokokin Jihar Kaduna ta amince da kudirin samar da kungiyar masu amfani da ruwan sha da makamantan su na 2025 ya zama doka.

Kudirin wanda zai bunkasa samar da ruwan sha da amfani a fadin jihar, ya samu karbuwa da amincewa cikin gaggawa saboda muhimmancin ruwa ga rayuwar al’umma.

Shugaban majalisar dokoki ta jihar, Yusuf Dahiru Liman ya sanar da amincewa da kudiring a lokacin zaman majalisar a Kaduna.

Kudirin da bangaren zartarwa na jihar ya aike da shi majalisar, an mika shi ga kwamitin ayyukan al’umma da samar da ababen more rdayuwa domin yin nazari akai, inda daga bisani ‘yan kwamitin suka tuntubi masu ruwa da tsaki a bangaren domin jin ba’asin su, sannan ya gabatar da bayanan da ya tattara da kuma shawarwari a zauren majalisar.

Shugaban kwamitin ayyukan al’umma da ababen more rayuwa, Alhaji Nasir Idris ya yi bayanin alfanun kudirin wajen bunkasa albarkatun ruwa a jihar da ma kasa baki daya.

Alhaji Nasir Idris ya lura cewa an amince da kudirin ne cikin hanzari duba da muhimmancin ruwa, wanda ya kasance wajen inganta lafiyar al’umma da zamantakewar su a jihar.

A wani labarin kuma, majalisar dokoki ta jihar Kaduna ta karba tare da amince da rahoton korafin da aka gabatar mata akan wani dan kwangila da aka baiwa aikin gina kasuwar Tudun Saibu ta Zamani a karamar hokumar Soba ta Jihar.

Da yake gabatar da rahoton binciken, Shugaban kwamitin bunkasa kasuwanni kuma dan majalisar mai wakiltar mazabar Jama’a, Mr. Ali Kalat aikin hadin gwiwa ne tsakanin majalisar karamar hukumar soba da wani kamfani Bebeji Integrated Services Limited wanda dan kwangilar ya gaza cika alkawarin da aka yi da shi,

A cewar rahoton, an kulla yarjejeniyar ce tun a watan Afrilun 2021 sannan a na sa ran kammalawa cikin kwanaki 90, sai dai dan kwangilar ya rushe gine-ginen tsohuwar kasuwar ce kawai ba tare da aza harsashin gina wata ba, duk da ikirarin da ya yi na cewa ya kai bulo 30,000 da siminti rabin tirela.

Kwamitin ya gano dan kwangilar ya saba yarjejeniya sannan ya bada shawarar a soke kwangilar domin a ba wani da ya cancanta domin gudanar da aikin.

Daga karshe kafatalin ‘yan majalisar sun amince da rahoton da kuma shawarwarin kwamitin.

Shamsuddeen Mannir Atiku

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Gudanar Da Taron Zaman Lafiya Tsakanin Manoma Da Makiyaya
  • Iran: Akwai damammaki na diflomasiyya da za mu jarraba aniyar Amurka a kansu
  • Tawagogin gwamnatin Kongo da kungiyar M23 sun isa  Doha domin tattaunawa
  • Namibiya ta janye bizar shiga ga wasu manyan kasashe na duniya
  • Gwamnatin Kano ta tura tawaga zuwa Edo kan kisan mafarauta
  • Amurka ta laftawa Iran sabbin takunkumai gabanin tattaunawar Oman
  • Sharhin Bayan Labarai: Yakin Kasuwanci Tsakanin Amurka da Kasashen Duniya
  • Tarayyar Turai Ta Yi Maraba Da Tattaunawa Tsakanin IRAN da Amurka Kan Shirinta Na Makamashin Nukliya
  • Majalisar Jihar Kaduna Ta Bude Bincike Kan Ginin Kasuwa da Aka Yi Watsi da Shi
  • Rahoto : Amurka za ta iya janye sojoji 10,000 daga Tsakiyar Turai