Aminiya:
2025-04-12@07:07:53 GMT

Ainihin abin da ke kawo wa Manchester United koma baya

Published: 11th, March 2025 GMT

An kora Kungiyar Kwallon Kafa ta Manchester United gida a Gasar cin Kofin FA na bana, bayan Fulham ta doke ta da ci 2-1 har gida a filin wasanta na Old Trafford a makon da ya wuce.

Manchester United ta yi bankwana da gasar ne alhali ita ce ke mai riƙe da Kofin FA da ta lashe a bara, bayan nasara a kan Manchester City, lamarin da ya ba ta damar buga Gasar Europa a kakar bana.

‘Yarjejeniyar sayar wa Matatar Dangote ɗanyen mai a farashin naira za ta ƙare a ƙarshen Maris’ An hana tashe bana a Kano — Nalako

Kungiyar Old Trafford ta koma matsayi na 14 a kasan teburin Firimiya da maki 34, bayan da ta ci wasanni tara da canjaras bakwai aka doke ta fafatawa 12.

Shekara 51 ke nan rabon da Manchester United ta yi irin wannan rashin ƙoƙarin, tun 1974 da ta faɗi daga babbar gasar tamaula ta Ingila.

Ta zama ’yar kallo a Gasar Firimiya Kofin Firimiya na karshe da ta dauka tun Kakar 2012/13, wanda shi ne karonta na 20 lokacin da Manchester City ta zo a matsayi na biyu da tazarar maki 11.

Daga nan Manchester City ta karɓe ragamar lashe babbar gasar ta Ingila.

Chelsea ta dauki kofin sau biyu sai Leicester City mai daya, sannan Liberpool ta dauka a 2020.

Liverpool na shirin lashe Firimiya na bana, wanda ita samu zai zame mata karo na 20 jimilla, za ta yi kan-kan-kan da yawan wanda United ta dauka a tarihi.

A yanzu haka, Liverpool ce ta daya a kan teburin Firimiya na kakar nan da maki 70, sai Arsenal ta biyu mai maki 55.

Magoya bayanta sun yi bore

A halin yanzu Kofin Europa ne kaɗai ya rage da Man-U take fatan dauka, wanda idan hakan ya tabbata, zai ba ta damar sake buga Gasar Zakarun Turai a badi da zarar ta lashe shi.

To sai dai magoya bayan kungiyar na shirin yin zangazanga wa Glazers, duba da yadda kungiyar ke zama kurar baya a hankali.

Laifin Iyalan Glazer ne?

Magoya bayan suna zargin Iyalan Glazer, masu kungiyar, da zama ummul-aba’isin koma bayan kungiyar. Suna zargin Daraktan Kungiyar, Glazer, da gazawa wajen iya rike ma’aikata da rashin biyan su albashi da ya dace.

Sun bayyana cewa matakan da Iyalan Glazer suke dauka na neman durkusar da kungiyar, lamarin da ya sa ma’aikata cikin rashin tabbas, suke ta ajiye aiki.

Matakan sun hada da korar daruruwan ma’aikata da kuma yanke albashi da alawus-alawus din ma’aikata da tsoffin ’yan wasa da masu horas da kungiyar.

Sun kuma dakatar da biyan tsohon kocin kungiyar, Sa Alex Ferguson, wanda ya jagoranci kungiyar ta lashe Kofin Firimiya guda 13.

Ba ’yan wasa ba ne matsalar — Amorin

A nasa bangaren kuma mai horas da ’yan wansan kungiyar, Ruben Amorim ya yi jirwaye mai kamar wanka da cewa matsalar ba daga ’yan wasa ko shi mai horas da kuniyar ba ne.

A yayin hira da ’yan jarida bayan wasan da aka kora su gida daga FA Cup bayan bugun fanariti, Amorin, ya jaddada nagartar ’yan wasan kungiyar.

Amorin ya bayyana cewa ya kamata tawagar kwallon kafa ta kasar Ingila ta gayyaci dan wasan baya na kungiyar, Harry Maguire, wanda shi ne ya ci kwallo a wasan nasu na FA na karshe.

Maguire mai shekara 31, wanda ya buga wa Ingila wasa 64, yana daga cikin manyan ’yan wasan da kasar ba ta je da su gasar cin Kofin Nahiyar Turai (EURO 2024) a Jamus ba.

Ingila ta kai wasan karshe, amma ta yi rashin nasara da ci 2-1a hannun tawagar Sifaniya a cikin watan Yulin 2024.

Maguire, wanda Erik ten Hag ya karbe mukamin kyaftin daga wajensa a 2023, yana taka rawar gani a wasannin da Manchester United ke yi a kakar nan.

Shi ne ya ci Leicester City kwallo a FA Cup zagaye na huɗu da kuma zura kwallo a ragar Ipswich Town a Firimiya a watan jiya.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Firimiyar Ingila Iyalan Glazer

এছাড়াও পড়ুন:

Tarayyar Turai Ta Yi Maraba Da Tattaunawa Tsakanin IRAN da Amurka Kan Shirinta Na Makamashin Nukliya

Kungiyar tarayyar Turai ta yi maraba da tattaunawa tsakanin Amurka da JMI dangane da shirinta na makamashin Nukliya, tare da kara jaddada cewa hanyar diblomasiyya kadai ta rage don warware wannan matsalar.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa a halin yanzu dai kungiyar tarayyar ta Turai ta na ci gaba da takurawa JMI da takunkuman tattalin arziki, masu  tsanani, a lokaci guda tana fadar cewa hanyar Diblomasiyya ce kadai ta rage wajen warware matsalar shirin makamashin nukliya na kasar Iran, wanda ya tabbatar da fuska biyu na kasashen na Turai.

Labarin ya kara da cewa, wani mai magana da yawun kungiyar ta EU wanda kuma baya son a bayyana sunansa, ya fadawa kamfanin dillancin labaran IRNA na kasar Iran kan cewa, babu hanyar da ta rage wajen warware matsalar shirin makamashin nukliya na kasar Iran sai hanyar Diblomasiyya.

Ya kumakara dacewa kungiyar tana maraba da duk wani ci gaba a wannan bangharen. Mai maganan ya kara da cewa wakilin EU a MDD ya yi wannan bayanin a gaban kwamitin tsaro na MDD a yan kwanakin da suka gabata.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • UBEC Ta Bayyana Jihar Jigawa A Matsayin Abin Kuyi A Fannin Ilimi
  • Tawagogin gwamnatin Kongo da kungiyar M23 sun isa  Doha domin tattaunawa
  • Ruwan Sama Ya Lalata Gidaje Sama Da 240 A Kebbi
  • Karin Harajin Amurka: Kaikayi Zai Koma Kan Mashekiya
  • Sojojin Sama Na HKI Kimani 1000 Guda New Suka Bukaci A Kawo Karshen Yaki A Gaza
  • Sin Ta Nuna Damuwa Kan Mummunan Tasirin Harajin Kwastam Na Amurka A Taron WTO
  • Ruwan sama ya lalata gidaje da yawa a Kebbi
  • Man City ta nace wa Guimaraes, Chelsea na son Rodrygo
  • Tarayyar Turai Ta Yi Maraba Da Tattaunawa Tsakanin IRAN da Amurka Kan Shirinta Na Makamashin Nukliya
  • Abinda Ya Kamata Kusani Akan Wasan Barcelona Da Borrusia Dortmund