Rahoto: Hare-haren jiragen yaki marasa matuka sun kashe daruruwan fararen hula a Afirka
Published: 11th, March 2025 GMT
Kimanin fararen hula 1,000 ne aka kashe tare da jikkata wasu daruruwa a hare-haren jiragen yaki marasa matuki a nahiyar Afirka, yayin da ake ci gaba da yin amfani da jirage marasa matuka a nahiyar.
A cewar jaridar The Guardian, masu sharhi da nazari na cewa , daga shekara ta 2021 zuwa 2024, jami’an tsaro a kasashe daban-daban na nahiyar Afirka sun yi amfani da jiragen yaki marasa matuka wajen kai hare-hare, wanda kuma sau tari ana kashe fararen hula ne, maimakon masu aikata laifuka.
Dole ne wannan ya kawo karshe, kuma dole ne kasashen duniya su dauki matakai da suka dace waje saka kaidoji kan amfani da jiragen yaki marasa matuka, domin rashin yin hakan zai ci gaba da yin sanadin salwantar rayukan fararen hula da basu bas u gani ba, in ji Cora Morris, jami’a a cibiyar sanya ido kan amfani da makamai ba bisa ka’ida ba da ke da mazauni a Burtaniya..
An tabbatar da cewa jirage marasa matuka masu dauke da makamai sun kashe fararen hula a kasashen Afirka masu yawa sakamakon tashe-tashen hankula, da hakan ya hada da kasashen Sudan, Somalia, Nigeria, Mali, Burkina Faso, da Habasha, inda akasarin hare-hare sun faruwa ne a wadannan yankuna.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: jiragen yaki marasa marasa matuka fararen hula
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan bindiga sun mamaye garuruwa 64 a Filato — Gwamna Mutfwang
Gwamna Caleb Mutfwang ya bayyana damuwa kan yadda matsalar tsaro ta ƙara ƙamari, yana mai cewa a halin yanzu ’yan bindiga sun mamaye aƙalla garuruwa 64 na Jihar Filato.
A wata hirarsa da gidan talabijin na Channels a yau Laraba, Gwamna Mutfwang ya ɗora alhakin matsalar tsaron da ake fuskanta a jiharsa kacokam a kan ta’addancin ’yan bindiga da ke ƙara ta’azzara.
Ibas ya naɗa kantomomin ƙananan hukumomin Ribas ’Yan bindiga sun kashe masunta 3 a SakkwatoGwamnan ya yi zargin cewa akwai masu ɗaukar nauyin hare-haren da ke aukuwa a jiharsa.
“A haƙiƙanin gaskiya babu wani bayani da zan yi face cewa akwai masu ɗaukar nauyin ta’addancin nan,” a cewar gwamnan.
“Abin tambayar shi ne, su wa ke ɗaukar nauyin ta’addancin? Wannan shi ne abin da hukumomin tsaro za su yi ƙoƙari su gano.
“Mun zo gaɓar da za a gano masu hannu a wannan lamari domin dole akwai masu ɗaukar nauyin waɗannan hare-haren.
“Waɗannan garuruwa da a bayan nan aka kai wa hari suna cikin yankunan da suka fuskanci hare-hare a 2023 amma suka sake gina alaƙaryar da kansu.
“Misali, a shekarar 2023 an kai wa ƙauyen Ruwi hari har aka kashe mutane 17, amma suka sake farfaɗowa suka gina matsugunninsu.
“Idan an ɗauki kusan shekaru 10 ana wannan hare-hare, shi yake nuna cewa akwai wasu da ke shirya wannan ta’addanci da gayya domin kawar da mutane daga doron ƙasa.
“A halin yanzu akwai aƙalla garuruwa 64 da ’yan bindiga suka mamaye a tsakanin ƙananan hukumomin Bokkos, Barkin Ladi, da Riyom na Jihar Filato.
“’Yan bindiga sun ƙwace iko waɗannan wurare sun sauya musu suna kuma mutane sun ci gaba da rayuwa a cikinsu.
“Sai dai ina fatan cewa nan da wani lokaci kaɗan hukumomin tsaro za su haɗa gwiwa domin kawo ƙarshen wannan matsalar.
Aminiya ta ruwaito cewa a makon jiya ne Gwamna Mutfwang ya yi iƙirarin cewa matsalar tsaron da ke addabar jihar ta wuce iya rikicin makiyaya da manoma.
“Dole ne na nanata cewa manufar waɗannan maƙiya ita ce tayar da hargitsi da hana zaman lafiya a jihar nan.
“Sai dai ba za mu yi ƙasa a gwiwa ba har sai mun tabbatar da cewa burinsu bai cika ba.
“Masu tunanin cewa rikicin makiyaya da manoma ne ka haddasa matsalar tsaro su daina wannan tunani domin kuwa wasu ne ke sojan gona da zummar hana zaman lafiya a jihar.
“Ina mai tabbatar wa mutanen Filato cewa da izinin Allah za mu yi nasara a kansu kuma mun kusa ganin ƙarshen waɗannan maƙiya,” a cewar gwamnan.