Aminiya:
2025-03-12@06:36:44 GMT

Jihohi 12 da za a fuskanci tsananin zafin rana — NiMet

Published: 11th, March 2025 GMT

Hukumar kula da yanayi ta Nijeriya NiMet ta yi gargaɗin cewa akwai yiwuwar a fuskanci tsananin zafin rana a wasu jihohin ƙasar na tsawon kwanaki huɗu.

Wata sanarwa da Nimet ta fitar ranar Litinin a Abuja, ta ce mutane su guji fita cikin tsananin zafi musamman daga karfe 12 na rana zuwa karfe 3.

Ainihin abin da ke kawo wa Manchester United koma baya ‘Yarjejeniyar sayar wa Matatar Dangote ɗanyen mai a farashin naira za ta ƙare a ƙarshen Maris’

Hukumar ta ce mutane za su ji sauyin al’amura a tsawon lokacin da za a kwashe ana tsala zafin ranar.

Jihohin da aka yi hasashen za su fuskanci ƙaruwar yanayi na zafin rana sun haɗa da Neja da Kwara da Oyo da Kogi da Nasarawa da kuma Benue.

Sauran sun haɗa da Enugu da Anambra da Abia da Ebonyi da Cross River da birnin tarayya Abuja.

NiMet ta ce wasu jihohin da ka iya fuskantar wannan barazana sun hada da Taraba da Adamawa da Filato da Kaduna da Zamfara da kuma Sakkwato.

Ta kuma shawarci al’umma da su riƙa shan isasshen ruwa a tsawon lokacin – su kuma yi amfani da fanka da na’urar sanyaya ɗaki da kuma zama a wurare masu inuwa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Zafin rana

এছাড়াও পড়ুন:

NAJERIYA A YAU: Abubuwan Da ke Shirin Faruwa A Fagen Siyasar Najeriya

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Fagen siyasar Najeriya na ci gaba da ɗaukar salo iri-iri yayin da ’yan kasa da dama suka yi kasaƙe suna jiran girgiza ta gaba wadda wasu suke ganin tsohon Gwamnan Jihar Kaduna Malam Nasir El-Rufai, ya ɗiga mata ɗanba.

A baya-bayan nan dai an yi ta tsegunguma da rade-radi a kana bin da wasu jiga-jigan ’yan siyasar ƙasar nan, musamman ’yan adawa da ’ya’yan jam’iyya mai mulki waɗanda suke takun saƙa da Shugaba Bola Ahmed Tinubu suke ƙullawa

Yanzu ta fara wari, an ji Malam Nasiru ya bayar da sanarwar ficewarsa daga jam’iyyar APC da tsallakawa zuwa SDP.

NAJERIYA A YAU: Ladan Da Mai Aikin Ƙarfi Yake Samu A Lokacin Azumi DAGA LARABA: Yadda Zawarawa Suke Ɗanɗana Kuɗa A Watan Ramadana

Shin ko me zai biyo bayan wannan girgiza da tsallen baɗaken Malam Nasiru da dirarsa suka haifar?

Wannan ne batun da shirin Najeriya a Yau na wannan lokaci zai duba.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • EFCC Ta Kama ‘Yan China 4, Da Wasu Mutum 27 Kan Zargin Hakar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Jos
  •  Ukraniya Ta Hai Wa Birnin Moscow Hari Da Jirage Marasa Matuki
  • Ana fargabar ɓarkewar Sanƙarau a Sakkwato
  • Lakurawa sun kashe mutum 13 a ƙauyukan Kebbi
  • Zafin Rana Zai Tsananta A Wasu Jihohin Nijeriya – NiMet
  • NAJERIYA A YAU: Abubuwan Da ke Shirin Faruwa A Fagen Siyasar Najeriya
  • ’Yan bindiga sun kashe manoma 14 a Ondo
  • New York Times: Isra’ila ce ta kashe wasu fursunoninta da ake tsare da su a Gaza
  • An harbe shugaban ƙungiyar Miyetti Allah a Kwara