Ana fargabar ɓarkewar Sanƙarau a Sakkwato
Published: 11th, March 2025 GMT
An gargaɗi mazauna da su kwana cikin shirin daƙile yaɗuwa cutar Sanƙarau a yayin da cututtuka masu alaƙa da ita suka soma bayyana a wasu ƙananan hukumomin Jihar Sakkwato.
Kwamishinan Lafiya na jihar, Dakta Faruk Umar Wurno ne ya yi wannan gargaɗi haɗi da bayar da shawarar a wani jawabi da ya fitar a ranar Talata.
Kwamishinan ya yi bayanin cewa ya zama wajibi duk wasu alamomi da aka gani a ɗauka a shiga da su ɗakin gwaje-gwaje a bincika domin a tabbatar ko ƙoshin lafiyar al’umma.
Dakta Faruk Umar ya ce ma’aikatarsa za ta saka ido kan jami’an lafiya na gwamnati da masu zaman kansu domin a tabbatar an daƙile yaɗuwar cutar.
Ya gargaɗi mazauna cewa a koyaushe su kasance a ankare wurin ɗaukar matakin kariya ga cututtuka na yau da kullum.
Ya buƙaci jama’a su riƙa gaggauta sanar da jami’an kiwon lafiya mafi kusa da zarar sun ga wata alama ta rashin lafiya kamar zazzaɓi ko ciwon kai mai tsanani.
Kwamishinan ya nanata muhimmancin tabbatar da tsaftar jiki da muhalli sannan jama’a su yi iya ƙoƙari wajen kaucewa shiga cunkoso da zama a wurin da iska ta wadata.
Ya buƙaci jama’a da su kai rahoton duk wata alama ta cuta ko wata rashin lafiya da ba a saba da ita ba a asibiti mafi kusa.
A kwanakin dai zafi yana tsananta a wasu jihohin ƙasar ciki har da Sakkwato, lamarin da babu shakka yana da nasaba da haddasa yaɗuwar cutar ta Sanƙarau.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Jihar Sakkwato Sanƙarau
এছাড়াও পড়ুন:
Cutar Kwastomomi: NERC ta ci kamfanonin rarraba lantarki tarar N628m
Hukumar Kula Wutar Lantarki ta Ƙasa (NERC) ta ci kamfanonin rarraba lantarki tarar naira miliyan 628 kan laifin karɓar kuɗin wuta fiye da kima daga hannun kwastomomi marasa mita.
Hukumar ta kuma ba wa kamfanonin rarraba lantarkin da hakan ta shafa wa’adin ranar 15 ga watan Mayu, 2025, sun tabbatar sun biya kwastomomin da suka canza fiye da kima, ta hanyar ba su wuta daidai da abin da suka ƙware su.
NERC ta bayyana cewa ɗaukar wannan mataki ya zama dole saboda kamfanonin sun yi kunnen ƙashi bayan umarnin da ta ba su, wanda ya ƙayyade kuɗin da su caji kwastomomi da ba su da mita.
Ta ce waɗanda aka ci tarar sun haɗa da Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Kaduna (Kaduna Electric) da Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Kano (KEDCO) da Kamfanin Rarraba Lantarki na Abuja (AEDC), Kamfanin Rarraba Lantarki na Jos da kuma Kamfanin Rarraba Lantarki na Yola.
Sauran su ne Kamfanin Rarraba Lantarki na Legas da takwarorinsa na Enugu da kuma Ikeja.
Sanarwar da Hukumar NERC ta fitar ta ce wannan tarar ta shafi kamfanonin guda takwas ne daga watan Yuli zuwa Satumbar shekarar 2024.
Ta bayyana cewa binciken da ta gudanar ya nuna kamfanonin sun yi watsi da umarnin nata da ya ƙayyade cazar kwastomomi marasa mita da ke kan layin lantarki guda a duk wata.