Aminiya:
2025-03-12@06:12:22 GMT

Ana fargabar ɓarkewar Sanƙarau a Sakkwato

Published: 11th, March 2025 GMT

An gargaɗi mazauna da su kwana cikin shirin daƙile yaɗuwa cutar Sanƙarau a yayin da cututtuka masu alaƙa da ita suka soma bayyana a wasu ƙananan hukumomin Jihar Sakkwato.

Kwamishinan Lafiya na jihar, Dakta Faruk Umar Wurno ne ya yi wannan gargaɗi haɗi da bayar da shawarar a wani jawabi da ya fitar a ranar Talata.

Lakurawa sun kashe mutum 13 a ƙauyukan Kebbi Tsohon shugaban Philippines ya faɗa komar ’yan sanda

Kwamishinan ya yi bayanin cewa ya zama wajibi duk wasu alamomi da aka gani a ɗauka a shiga da su ɗakin gwaje-gwaje a bincika domin a tabbatar ko ƙoshin lafiyar al’umma.

Dakta Faruk Umar ya ce ma’aikatarsa za ta saka ido kan jami’an lafiya na gwamnati da masu zaman kansu domin a tabbatar an daƙile yaɗuwar cutar.

Ya gargaɗi mazauna cewa a koyaushe su kasance a ankare wurin ɗaukar matakin kariya ga cututtuka na yau da kullum.

Ya buƙaci jama’a su riƙa gaggauta sanar da jami’an kiwon lafiya mafi kusa da zarar sun ga wata alama ta rashin lafiya kamar zazzaɓi ko ciwon kai mai tsanani.

Kwamishinan ya nanata muhimmancin tabbatar da tsaftar jiki da muhalli sannan jama’a su yi iya ƙoƙari wajen kaucewa shiga cunkoso da zama a wurin da iska ta wadata.

Ya buƙaci jama’a da su kai rahoton duk wata alama ta cuta ko wata rashin lafiya da ba a saba da ita ba a asibiti mafi kusa.

A kwanakin dai zafi yana tsananta a wasu jihohin ƙasar ciki har da Sakkwato, lamarin da babu shakka yana da nasaba da haddasa yaɗuwar cutar ta Sanƙarau.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Sakkwato Sanƙarau

এছাড়াও পড়ুন:

Yadda Al’ummar Kasar Sin Ke Tabbatar Da Hakkinsu Na Demokuradiyya 

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • EU ta jadadda bukatar warware batun Iran ta hanyar diflomasiyya
  • EFCC Ta Kama ‘Yan China 4, Da Wasu Mutum 27 Kan Zargin Hakar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Jos
  • Sanƙarau ta kashe mutum 26 a Kebbi
  • Yadda Al’ummar Kasar Sin Ke Tabbatar Da Hakkinsu Na Demokuradiyya 
  • Sheikh Qassem: Duk da wahalhalun, Hizbullah tana da karfinta
  • Iyalan Abacha sun gargaɗi Babangida kan ɓata sunan mahaifinsu
  • Ramadan: Ali JC ya bai wa jama’a tallafin kayan abinci a Gombe
  • Iran, Rasha da China, sun fara wani atisayin sojojin ruwa a kusa da tashar ruwa ta Chabahar
  • WHO Za Ta Bai Wa Najeriya Magungunan Cutar Kuturta