A Cikin Shekara Daya EFCC Ta Kwato Dalar Amurka Miliyan 500
Published: 11th, March 2025 GMT
Hukumar da take fada da yi wa tattalin arzikin kasar Najeriya ta’annatii ta kwato da kudaden da sun kusa dalar Amurka miliyan 500. Haka nan kuma hukumar ta kwato man fetur da sauran dangoginsa da sun kai ton 931,000, sai kuma gidajen da sun kai 975.
A cikin rahoton da ta fitar a ranar litinin hukumar ta EFCC ta bayyana cewa, ta sa an hukunta masu laifi har su 4,000 wanda shi ne adadi mafi girma tun kafa ta.
Tuni an zuba wasu kudaden da aka kwato a cikin ayyukan gwamnati.
A karshen rahoton hukumar “Transparency International” ta bayyana Najeriya a matsayin kasa ta 140, a jerin masu fama da cin hanci da rashawa, bayan da a baya ta kasance ta 180.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
NAJERIYA A YAU: Tasirin ’Yan Uwantaka Ga Rayuwar Al’umma
More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba
Irin alaƙar da ke tsakanin wasu abokai na da matuƙar kusanci da kyau, ta yadda a wasu lokutan ma ba a iya banbance dangantakar tsakaninsu ta ’yan uwan na jini ko kuma abota.
Irin wannan dangantaka ya kamata ne a ce ana samun ta a tsakanin ’yan uwa na jini.
Sai dai a yayin da wasu ke samun kyakkyawan dangantaka tsakaninsu da ’yan uwan su na jini, wasu kuwa ba sa ga-maciji da nasu ’yan uwan da suke uwa ɗaya uba ɗaya.
NAJERIYA A YAU: Dabarun Samun Kuɗaɗe Ta Hanyar Amfani Da Wayar Hannu DAGA LARABA: Abin Da Ya Sa ‘Matar Bahaushe Ba Ta Iya Kiran Sunan Mijinta’Shirin Najeriya A Yau na wannan rana zai yi nazari ne kan irin tasirin da ’yan uwantaka ke da shi ga rayuwar mutum.
Domin sauke shirin, latsa nan