HausaTv:
2025-03-12@06:31:30 GMT

A Cikin Shekara Daya EFCC Ta Kwato Dalar Amurka Miliyan 500

Published: 11th, March 2025 GMT

Hukumar da take fada da yi wa tattalin arzikin kasar Najeriya ta’annatii ta kwato da kudaden da sun kusa dalar Amurka miliyan 500. Haka nan kuma hukumar ta kwato man fetur da  sauran dangoginsa da sun kai  ton 931,000, sai kuma gidajen da sun kai 975.

A cikin rahoton da ta fitar a ranar litinin hukumar ta  EFCC ta bayyana cewa,  ta sa an hukunta masu laifi har su 4,000 wanda shi ne adadi mafi girma tun kafa ta.

Tuni an zuba wasu kudaden da aka kwato a cikin ayyukan gwamnati.

A karshen rahoton hukumar  “Transparency International” ta bayyana Najeriya a matsayin kasa ta 140, a jerin masu fama da cin hanci da rashawa, bayan da a baya ta kasance ta 180.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Kasancewar “Taiwan A Matsayin Lardin Kasar Sin” Shi Ne Matsayin MDD A Ko Yaushe 

Ministan harkokin wajen kasar Sin, Wang Yi ya bayyana a wajen taron manema labaru na ministan harkokin waje da aka shirya a harabar manyan tarukan kasar Sin guda biyu, lokacin da yake magana kan batun Taiwan cewa: suna daya tilo na Taiwan a Majalisar Dinkin Duniya shi ne “Lardin Taiwan na kasar Sin”. Kuma wasu sun yi amannar cewa, hakan ne ya sa manufar babban yankin kasar Sin a kan Taiwan ta zama mai tsaurin gaske.

Da take mayar da jawabi game da wannan batu, mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin, Mao Ning, ta bayyana a wani taron manema labarai da aka saba gudanarwa da ya gudana yau 10 ga wata cewa, wannan shi ne daidaitaccen matsayin MDD a ko yaushe kuma haka abun yake a tarihi.

Mao Ning ta jaddada cewa, a ko da yaushe kasar Sin tana bin ka’idar kasancewar Sin daya tak, da kuma ra’ayi daya da aka samu na shekarar 1992, kana tana matukar son yin kokari don ganin an samu damar dinkuwar kasar Sin cikin lumana da gaskiya da sa himma. A sa’i daya kuma, kasar Sin za ta dauki dukkan matakan da suka dace don kare ikon mallakar kasarta da cikakken ‘yancin yankinta, da kuma fitowa da kakkausan harshe wajen nuna adawa da ayyukan ‘yan aware na neman ‘yancin kai na Taiwan da tsoma baki daga waje. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Najeriya ta yi hasashen samun karuwar kashi 4.6 cikin dari na GDP a 2025
  • Matsin Amurka Ya Zama Zaburarwa Ga Kasar Sin Wajen Kara Samun Ci Gaba
  • Majalisar Dokokin Kasar Sin Ta Rufe Zaman Taronta Na Shekara-shekara
  • NAJERIYA A YAU: Abubuwan Da ke Shirin Faruwa A Fagen Siyasar Najeriya
  • Kasancewar “Taiwan A Matsayin Lardin Kasar Sin” Shi Ne Matsayin MDD A Ko Yaushe 
  • Gina Mutane Don Bunkasa Hazakarsu Na Daga Cikin Ajendar Sin Na 2025
  • NAJERIYA A YAU: Ladan Da Mai Aikin Ƙarfi Yake Samu A Lokacin Azumi
  • DRC Ta Sa Kudi Dalar Amurka Miliyan 5 Akan Jagororin ‘Yan Tawayen M 23
  • WHO Za Ta Bai Wa Najeriya Magungunan Cutar Kuturta