“Yan Ta’addan Syria Suna Boye Gawawwakin Mutanen Da Su Ka Yi Wa Kisan Gilla
Published: 11th, March 2025 GMT
Rahotannin da suke fitowa daga Syria sun ambaci cewa kungiyoyin ‘yan ta’adda da suke da alaka da shugaban gwamnatin Syria, Julani sun fara dauke gawawwakin mutanen da su ka yi wa kisan kiyashi zuwa wasu wurare da ba a san ko’ina ne ba.
Saboda yadda fushin kasashen duniya yake karuwa akan kisan kiyashin da ‘yan ta’adda su ka yi a gabar ruwan Syria, masu mulki a Damascuss suna boye gawawwakin gabanin isar tawagar MDD zuwa yankin.
Mafi yawancin mutanen da aka yi wa kisan gillar a yankin gabar ruwan Syria, fararen hula ne wadanda aka fito da su daga cikin gidajensu,yayin da wasu kuma aka yi musu kisan gilla a gaban iyalansu.
Ya zuwa shekaran jiya ana maganar cewa an kashe mutanen da sun kai 1,700.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Harajin China da Amurka: Mene ne makomar tattalin arziƙin duniya?
Sabon rikici ya sake kunno kai tsakanin ƙasashen China da Amurka, yayin da shugaba Donald Trump, ya ƙara wa kayayyakin da ake shiga da su ƙasar daga China haraji zuwa kashi 104.
Wannan matakin ya shafi kayayyaki kamar wayoyin hannu, batir, kayan wasan yara da na’urorin wasanni.
Za a ci gaba da sayar da ɗanyen mai a farashin Naira — Gwamnati Likitocin Nijeriya dubu 16 sun yi ƙaura zuwa ƙetare — Ministan Lafiya China ta ce ba za ta zuba ido baChina ta bayyana cewa ba za ta zuba ido ta yi tagumi yayin da ake gallaza mata.
China ta mayar da martani da nata harajin kashi wanda ta ƙada zuwa kashi 34 kan kayayyakin Amurka, inda ta kuma ce tana shirin ƙara wani harajin.
Ta rage darajar kuɗinta (Yuan) domin ƙarfafa fitar da kayayyaki zuwa ƙasashen waje.
A lokaci guda kuma, ta fara bincike kan wasu manyan kamfanonin Amurka kamar Google, inda kuma ta ke shirin daƙile wasu muhimman albarkatu.
Masana tattalin arziƙi na gargaɗin cewa wannan rikici zai shafi ƙasashe da dama, musamman na nahiyar Asiya kamar Vietnam da Cambodia, waɗanda harajin zai shafa daga Amurka.
Ana kuma ganin cewa wannan zai iya janyo hauhawar farashin kayayyaki a Amurka da kuma raguwar sayayya daga China.
Wannan ba rikicin haraji ba ne – ƘwararruWasu ƙwararru sun bayyana cewa wannan ba kawai rikicin haraji ba ne, wata gwagwarmaya ce ta nuna iko a harkokin kasuwancin duniya.
Ko da yake tattalin arziƙin China na fuskantar tangarɗa a yanzu, amma masana na ganin tana iya ɗorewa, domin kauce wa nuna rauni ga matakin da Amurka ke kai mata.
A gefe guda kuwa, Amurka na fama da matsin lamba daga ‘yan kasuwa da masu zuba jari da ke jin tsoron sakamakon wannan rikici.
Masana na fargabar lokacin da rikicin zai ƙareMasana sun bayyana cewa da wuya a san yadda wannan rikici zai ƙare.
Amma ana fatan cewa shugabannin ƙasashen biyu za su zauna tattaunawa domin samun mafita.
Ƙasashen duniya na fargabar cewa idan ba a daidaita ba, rikicin na iya taɓa tattalin arzikin duniya gaba ɗaya.