“Yan Ta’addan Syria Suna Boye Gawawwakin Mutanen Da Su Ka Yi Wa Kisan Gilla
Published: 11th, March 2025 GMT
Rahotannin da suke fitowa daga Syria sun ambaci cewa kungiyoyin ‘yan ta’adda da suke da alaka da shugaban gwamnatin Syria, Julani sun fara dauke gawawwakin mutanen da su ka yi wa kisan kiyashi zuwa wasu wurare da ba a san ko’ina ne ba.
Saboda yadda fushin kasashen duniya yake karuwa akan kisan kiyashin da ‘yan ta’adda su ka yi a gabar ruwan Syria, masu mulki a Damascuss suna boye gawawwakin gabanin isar tawagar MDD zuwa yankin.
Mafi yawancin mutanen da aka yi wa kisan gillar a yankin gabar ruwan Syria, fararen hula ne wadanda aka fito da su daga cikin gidajensu,yayin da wasu kuma aka yi musu kisan gilla a gaban iyalansu.
Ya zuwa shekaran jiya ana maganar cewa an kashe mutanen da sun kai 1,700.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
El-Rufa’i ya sauya sheƙa daga APC zuwa SDP
Tsohon Gwamnan Kaduna, Nasir El-Rufa’i ya tabbatar da sauya sheƙa daga jam’iyyar APC mai mulkin ƙasar zuwa jam’iyyar SDP.
Hakan na ƙunshe cikin wata sanarwa da ya wallafa ranar Litinin ne a shafukansa na sada zumunta.
’Yan bindiga sun yi garkuwa da matashi a Kano Tsohon Mataimakin Gwamnan Kogi Patrick Adaba ya rasuEl-Rufai ya ce, “yanzu na yanke shawarar komawa jam’iyyar Social Democratic Party, kuma zan kasance a cikin ta wajen tafiyar da al’amurana na siyasa a nan gaba.
Kwanakin baya a lokacin tattaunawarsa da kafar talabijin ta Arise, El-Rufa’i ya bayyana cewa “jam’iyyar APC ta sauka daga kan manufofin da aka assasa ta tun fil-azal.”
Ya yi zargin cewa jam’iyyar ta gaza kiran taron shugabanninta na ƙasa tsawon shekaru, wanda ya ce hakan ya saɓa wa tanade-tanaden kundin tsarin mulkin jam’iyyar.
A yanzu dai wannan ya kawo ƙarshen raɗe-raɗin da ake yi na inda tsohon gwamnan zai nufa bayan raba gari da jam’iyyar APC.