Uganda Ta Aike Da Sojoji Zuwa Sudan Ta Kudun Domin Kare Babban Birnin Kasar
Published: 11th, March 2025 GMT
Kasar Uganda ta sanar da aikewa da sojojinta zuwa birnin birnin kasar Sudan Ta Kudu, Juba saboda ba shi kariya. Sai dai har yanzu gwamnatin Sudan din ba ta tabbatar da hakan ba.
Babban hafsan hafsoshin sojojin kasar Uganda Janar Muhoozi Kainerugaba ya bayyana cewa; Rundunar musamman ta Ugandan ta shiga cikin birnin Juba, domin ba shi kariya.
Janar Muhoozi Kainerugaba ya kuma ce: “ Za mu kare dukkanin kasar Sudan Ta Kudu, kamar yadda za mu kare kasarmu. A wurinmu Salva Kiir ne mu ka aminta da cewa halartaccen shugaban kasar Sudan Ta Kudu,don haka duk wanda zai shelanta yaki akansa, ya shelanta yaki ne akan Uganda.”
Har ila yau janar din na Uganda ya kuma ce; “ Wadanda su ka aikata laifuka za su dandana kudarsu.”
A cikin kwanakin bayan nan an shiga dambaruwar siyasa a kasar Sudan Ta Kudu bayan da gwamnatin shugaban Salva Kiir ta kama jami’an soja da kuma na siyasa masu alaka da mataimakin shugaban kasar Reik Machar. Hakan ya biyo bayan barkewar wani sabon bore ne na ‘yan kabilar Nuer da su ka yi fada da sojojin gwamnati.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kasar Sudan
এছাড়াও পড়ুন:
Sojojin Kasar Yamen Sun Maida Martani Ga Hare-Haren Amurka Kan Amurkan Da Kuma HKI
Sojojin kasar Yamen sun bada sanarwan maida martani ga hare-haren jiragen yakin kasar Amurka a kan kasar na baya-bayan nan, kuma zasu ci gaba da kai hare-haren kan wadannan wurare har zuwa lokacinda za’a kawo karshen yaki a Gaza.
Tashar talabijin ta presstv a nan Tehran ta nakalto kakakin sojojin kasar Yemen Burgediya Janar Yahyah Saree yana fadar haka a yau Laraba . Ya kuma kara da cewa, a wannan karon sun yi amfani da jiragen yaki wadanda ake sarrafasu daga nesa, kan wasu wurare masu muhimmanci a birnin Yaffa (tel’aviv). Haka ma sun cilla wasu makaman kan jirgin yaki mai daukar jiragen sama na Amurka wato USS Harry Truman dake arewacin tekun red Sea.
Kafin haka dai jiragen Amurka wadanda suke tasowa daga jiragin yaki USS Harry Truman sun kai hare-hare kan wurare daban daban a kan kasar ta Yemen.
Tun cikin watan Octoban shekara ta 2023 ne sojojin kasar Yemen suka shiga yaki da kuma HKI da kasashen da suke tallafa mata, saboda tallafa wa falasdinawa a Gaza wadanda sojojin HKI take masu kissan gilla tun lokacin.
Gwamnatin kasar Amurka ta bada sanarwan kafa kawance ta tabbar da amincin jiragen kasuwanci na HKI a cikin tekun Red sea amma ta kasa samar da aminci ga jiragen HKI a ko masu zuwa wajenta a tekun har yanzu.