Aminiya:
2025-03-12@12:07:30 GMT

Manyan makarantu sun shiga yajin aiki a Adamawa

Published: 11th, March 2025 GMT

Gamayyar ƙungiyoyin manyan makarantu na gwamnatin Jihar Adamawa sun tsunduma yajin aikin sai baba ta gani a yau Talata, 11 ga watan Maris.

Ma’aikatan manyan makarantun da suka haɗa da masu karantarwa da waɗanda ba sa karantarwa sun shiga yajin aiki ne bayan wa’adin yajin aikin gargaɗi na kwanaki bakwai da ya ƙare a jiya Litinin.

Sanƙarau ta kashe mutum 26 a Kebbi Ana fargabar ɓarkewar Sanƙarau a Sakkwato

Cikin wata sanarwa da shugaba, Maryam Abdullahi da kuma sakataren ƙungiyoyin, Kwamared Musa Yakubu suka sanyawa hannu, sun alaƙanta yajin aikin a matsayin martani da halin ko-in-kula da gwamnatin jihar ta nuna kan buƙatunsu.

Dangane da hakan gamayyar ƙungiyoyin ke kiran dukkan mambobinta da su tsunduma yajin aikin na sai baba ta gani.

Aminiya ta ruwaito cewa, yajin aikin ya shafi manyan makarantu daban-daban ciki har da kwalejojin ilimi da fasaha da na lafiya da ke faɗin Jihar Adamawa.

Ƙungiyoyin dai na neman gwamnatin ta mayar da mambobinsu kan tsarin albashin manyan makarantu da kuma tsarin sabon albashi mafi ƙanƙanta da kuma janye tsarin zaftare albashinsu da ake yi da sunan haraji.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Adamawa manyan makarantu Yajin aiki manyan makarantu yajin aikin

এছাড়াও পড়ুন:

An cafke mutum uku kan satar wayoyin lantarki a Adamawa

’Yan sanda sun cafke wasu mutum uku bisa zargin lalatawa da kuma satar wayoyin lantarki a ƙauyen Bororo da ke Ƙaramar Hukumar Michika ta Jihar Adamawa.

An cafke ababen zargin ne da wayoyin lantarkin yayin wani sintiri da jami’an ’yan sanda suka gudanar a ranar 9 ga wannan wata na Maris.

Abin da ya sa na sauya sheƙa daga APC zuwa SDP — El-Rufai ’Yan bindiga sun yi garkuwa da matashi a Kano

Mai magana da yawun rundunar ’yan sandan, Suleiman Yahaya Nguroje, ya ce ababen zargin da ke hannu sun yi iƙirarin aikata laifin da ake zarginsu da shi.

Sai dai ya ce za a ci gaba da gudanar da bincike gabanin ɗaukar matakin da ya ce nan gaba kaɗan.

Kwamishinan ’yan sandan jihar, Dankombo Morris, ya yaba wa jami’an da suka yi ruwa da tsaki wajen cafke ababen zargin, yana mai jaddada aniyar ƙara ƙaimi wajen tsare dukiyoyin al’umma.

Rundunar ’yan sandan ta buƙaci mazauna da su ci gaba da ba ta haɗin kai wajen lura da duk wani motsi tare da kai rahoto duk wani abin zargi zuwa mahukunta mafi kusa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sabon Kwamishinan ‘Yansanda Ya Kama Aiki A Kano
  • Manyan Jami’o’in Kasar Sin Sun Fadada Daukar Dalibai A Fannin AI Da Manya Tsare-tsare
  • Sin Ta Gaggauta Aikin Gyara Da Kyautata Ababen Aikin Gona
  • Kamfanin Kasar Sin Zai Gudanar Da Aikin Farfado Da Muhallin Halittu Na Kogin Nairobi Na Kasar Kenya
  • Sojojin Ruwa Na Kasashen Rasha Da China Sun Shigo Kasar Iran Don Fara Atisayen Sojojin Ruwa Mai Suna “Damarar Tsaro 2025”
  • Gwamnatin Kano Ta Bullo Da Sabbin Hanyoyin Kare Makarantunta Daga Kalubalen Tsaro
  • An cafke mutum uku kan satar wayoyin lantarki a Adamawa
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Alhinin Rasuwar Fitaccen Masanin Aikin Jarida, Kabir Ɗangogo
  • Mun bai wa Akpabio sa’o’i 48 ya dawo da Sanata Natasha — SERAP