Aminiya:
2025-04-12@07:15:19 GMT

Majalisar Wakilai ta ba da umarnin rufe shafukan intanet na batsa

Published: 11th, March 2025 GMT

Majalisar Wakilai ta bai wa Hukumar Sadarwa ta NCC umarnin rufe duk wasu shafukan intanet masu nuna batsa a Nijeriya.

Majalisar ta ba da wannan umarni yayin zamanta na yau Talata, inda ta nemi hukumar sadarwar ta umarci duk kamfanonin da ke samar da intanet su rufe duk wasu shafukan intanet da ke nuna hotuna ko bidiyon batsa cikin gaggawa.

Manyan makarantu sun shiga yajin aiki a Adamawa Sanƙarau ta kashe mutum 26 a Kebbi

Wannan umarni na zuwa ne bayan wani ƙudiri da ɗan majalisa daga Jihar Katsina, Dalhatu Shehu Tafoki, ya gabatar.

Tafoki ya bayyana cewa bidiyoyin batsa da ke intanet na zama babbar matsala a duniya, kuma zuwa yanzu Nijeriya ba ta ɗauki wani matakin magance matsalar ba.

Ya kafa hujjar cewa Nijeriya ƙasa ce mai addini, inda manyan addinan ƙasar suka haramta batsa da kuma nuna tsiraici.

Tafoki ya kuma bayyana gargaɗin da masana halayyar ɗan Adam suka yi kan mummunan tasirin da kallon bidiyon batsa ke da shi, ciki har da yiwuwar kusantar zina, da karuwanci, da kuma kasa rabuwa da kallon.

Majalisar ta kuma buƙaci hukumar NCC ta hukunta duk kamfanin samar da intanet da ya bijirewa wannan umarnin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Majalisar Wakilai tsiraici

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Lawal Ya Yi Jimamin Rasuwar Ɗan Majalisar Zamfara, Aminu K/Daji

“Ina rokon Allah Maɗaukakin Sarki Ya gafarta masa, ya sa ya huta har abada.”

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Amurka Ta Sayi Kayayyakin Nijeriya Na Dala Miliyan 643 A Wata 2 – Rahoto
  • An Kaddamar Da Bikin Nuna Fina-Finan Sinanci Na CMG Karo Na 5
  • Trust Radio 92.7FM za ta fara shirye-shiryen gwaji
  • Sin Ta Nuna Damuwa Kan Mummunan Tasirin Harajin Kwastam Na Amurka A Taron WTO
  • Yadda masu safarar ɗan Adam ke yaudarar mutane ta intanet
  • Majalisar Kano Ta Yi Murna Da Lambar Yabo Da Jaridar LEADERSHIP Ta Bai Wa Abba
  • Gwamnan Zamfara Ya Yi Jajen Rasuwar Dan Majalisa Aminu K/Daji
  • Gwamna Lawal Ya Yi Jimamin Rasuwar Ɗan Majalisar Zamfara, Aminu K/Daji
  • Gwamnan Zamfara Ya Yi Jimamin Rasuwar Ɗan Majalisar Zamfara, Aminu K/Daji
  • Majalisar Jihar Kaduna Ta Bude Bincike Kan Ginin Kasuwa da Aka Yi Watsi da Shi