Leadership News Hausa:
2025-04-12@07:13:10 GMT

Sin Ta Gaggauta Aikin Gyara Da Kyautata Ababen Aikin Gona

Published: 12th, March 2025 GMT

Sin Ta Gaggauta Aikin Gyara Da Kyautata Ababen Aikin Gona

Jiya Litinin, kwamitin raya kasa da yin kwaskwarima na kasar Sin ya sanar da cewa, a bana, kasar Sin za ta gaggauta aikin gyara da kyautata ababen aikin gona a muhimman yankunan shuka kayan lambu cikin manyan rumfuna.

A matsayin muhimmin matakin kara bukatun al’umma da karfafa bunkasar tattalin arziki, majalisar gudanarwar kasar Sin ta fara aikin kyautata na’urorin aiki da kuma maye gurbin tsoffin kayayyaki da sabbabi a bara.

A bana kuma, an habaka wannan aiki zuwa harkar noma, inda za a mai da hankali wajen gyara da kyautata tsoffin manyan rumfuna masu aiki da hasken rana, da rumfuna na roba, domin karfafa tsarin kiyaye tsaro, da kara yin amfani da gonaki.

Haka kuma, bisa wannan shiri, za a kyautata da kuma samar da na’urorin zamani, kamar na’urar daidaita yanayi cikin rumfa, da na’urar samar da ruwa da taki mai sarrafa kanta da dai sauransu, ta yadda za a kara yin amfani da manyan injunan aikin gona masu sarrafa kansu, yayin da tabbatar da dauwamammen ci gaban aikin gona. (Mai Fassara: Maryam Yang)

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Hizbullah ta kirayi gwamnatin Lebanon da ta dauki mataki kan hare-haren Isra’ila

Wakilin kungiyar Hizbullah a majalisar dokokin kasar Labanon ya yi kira ga gwamnatin kasar da ta ba da fifiko wajen dakatar da hare-haren wuce gona da iri da gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ke yi wa kasar Labanon.

A cewar Al-Mayadeen Hassan Fadlallah mamba a bangaren Hizbullah a majalisar dokokin kasar Labanon ya ce: Dakatar da wuce gona da iri kan kasar Labanon wani muhimmin al’amari ne na kasa da ya zama wajibi a sanya shi cikin ajandar gwamnatin Lebanon.

Ya kara da cewa: Al’ummar kasar Labanon suna fuskantar wuce gona da iri na gwamnatin sahyoniyawan tare da yin kira ga gwamnati da ta sauke nauyin da ya rataya a wuyanta na dakile wannan ta’addanci.

Fadlallah dai ya dauki babbar matsalar kasar Labanon a matsayin mamaya da kuma keta hurumin kasar, yana mai jaddada cewa wasu na son jefa kasar cikin rudani da ruguza karfin da kasar ta Lebanon ke da shi na tunkarar mulkin kama-karya na kasashen waje. Irin wadannan ayyuka sun saba wa muradun kasar Lebanon, kuma sun yi daidai da muradin makiya.

Hassan Fadlallah ya musanta ikirarin da wasu kafafen yada labarai suka yi cewa Hizbullah na amfani da tashar jiragen ruwa na Beirut wajen safarar makamai, ya kuma yi kira ga mahukuntan kasar Lebanon da su dauki mataki kan masu yada wadannan karairayi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dalilin Nijeriya Na Karbo Bashin Dala Biliyan 12 Daga Kasar Japan
  • Namibiya ta janye bizar shiga ga wasu manyan kasashe na duniya
  • Hizbullah ta kirayi gwamnatin Lebanon da ta dauki mataki kan hare-haren Isra’ila
  • Ku Kyautata Rayuwar Jama’a Ba Taku Ba — Buhari Ga Gwamnonin APC
  • Ku Kyautata Rayuwar Jama’a Ba Kan Kanku Ba — Buhari Ga Gwamnonin APC
  • Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 10, Sun Kashe Ɗan Bindiga 1 A Katsina
  • Sin Ta Kara Wasu Kamfanonin Amurka 12 Cikin Jerin Wadanda Ta Dakatar Da Fitar Musu Da Wasu Kayayyaki Daga Kasar Sin
  • Hajjin 2025: Jihar Kaduna Ta Yi Tanadin Masauki Na Musamman Ga Alhazan Bana
  • Sin Ta Kara Buga Haraji Kan Kayayyakin Da Ake Shigarwa Kasar Daga Amurka Zuwa 84%
  • Zuba Jari Daga Kasashen Waje A Noman Zamani: Jigawa Ta Baje Kolin Aikin Noma A Abuja