Aminiya:
2025-04-12@07:16:05 GMT

’Yan bindiga sun yi garkuwa da fasinjoji 450 a Pakistan

Published: 12th, March 2025 GMT

Wasu ’yan bindiga sun yi garkuwa da daruruwan fasinjoji a ranar Talata a wani yunkurin ci gaba da ta da hankali da wata kungiyar ’yan aware ke yi a Kudu maso yammacin Pakistan.

’Yan bindigar sun raunata direban jirgin kasan a kokarinsu na kwace iko da jirgin a yankin Balochistan mai duwatsu da ke iyaka da Afghanistan da kuma Iran.

Majalisar Wakilai ta ba da umarnin rufe shafukan intanet na batsa Manyan makarantu sun shiga yajin aiki a Adamawa

Wani babban jami’in gwamnati mai kula da harkokin sufurin jiragen kasa Muhammad Kashif ya shaida wa AFP cewa adadin mutane da aka yi garkuwa da su ya kai 450.

Sai dai kuma shafin jaridar rnz na intanet ya ruwaito cewa, daga bisani an kubutar da akalla fasinjoji 100 yayin da ajali ya katse hanzarin wasu uku a yayin harin da ya auku a kudu maso gabashin Balochistan.

Kungiyar Baloch Liberation Army (BLA) mai yunkurin neman cin gashin kan yankin Balochistan, ta dauki alhakin garkuwar baya ga zargin hukumomi da mamaye arzikin yankin.

Kungiyar dai BLA ta dade ta na tayar da zaune tsaye a Pakistan kuma ta na ikirarin a bar mata yankunanta don rike madafun iko.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Jami’an Amurka da na Saudiyya sun tattauna batutuwan da suka shafi Gaza da yankin

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Amurka Tommy Bruce a cikin wata sanarwa da ya fitar ya bayyana cewa: Ministocin harkokin wajen Amurka da na Saudiyya sun tattauna kan yunkurin diflomasiyya a Gaza na sakin mutanen da aka yi garkuwa da su da kuma samar da tsagaita bude wuta mai dorewa a Gaza inda Hamas ta samu cikaken kwance damarar makamai da nakasassu.

An gudanar da taron ne a daidai lokacin da ake ci gaba da yin kiraye-kirayen a samar da mafita a siyasance a yakin Gaza, inda Isra’ila ta kashe Falasdinawa fararen hula fiye da 50,000 tun daga watan Oktoban 2023 (Bahan 1401).

A yayin da Amurka ke ci gaba da goyon bayan munanan hare-hare na gwamnatin sahyoniyawan da kuma kokarin shiga tsakani kan yarjejeniyar daidaita alaka tsakanin Saudiyya da gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila, Riyadh ta jaddada tsagaita bude wuta nan take a zirin Gaza da kuma hanyar samar da kasashe biyu.

A watan da ya gabata, shugaban Amurka Donald Trump ya ce watakila ya ziyarci Saudiyya tun a farkon wannan watan (Afrilu). A wa’adin farko na gwamnatin Trump a shekarar 2017, Saudiyya ita ce kasar farko da Trump ya fara zuwa kasashen waje. Duk da haka, Axios ya ruwaito cewa tafiya za ta faru a tsakiyar watan Mayu.

Ministocin harkokin wajen Amurka da na Saudiyya sun kuma tattauna kan wasu batutuwan yankin da suka hada da yakin Sudan da Yemen.

Sanarwar da ma’aikatar harkokin wajen Amurka ta fitar ta ce: Ministocin harkokin wajen Amurka da na Saudiyya sun kuma amince da cewa, sojojin kasar Sudan da dakarun da ke ba da goyon baya cikin gaggawa su koma kan teburin sulhu, da kare fararen hula, da bude kofofin jin kai, da kuma komawa ga farar hula.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rayuwar ‘Yan Arewa Na Cikin Hadari, Yayin Da Gurbataccen Gishiri Ya Fantsama A Kasuwanni
  • Tawagogin gwamnatin Kongo da kungiyar M23 sun isa  Doha domin tattaunawa
  • Gwamnati ta gargaɗi jihohi 30 kan ambaliyar ruwa
  • Sin Ta Nuna Damuwa Kan Mummunan Tasirin Harajin Kwastam Na Amurka A Taron WTO
  • An kama masu garkuwa da mutane biyu a Yobe
  • Jami’an Amurka da na Saudiyya sun tattauna batutuwan da suka shafi Gaza da yankin
  • Yadda masu safarar ɗan Adam ke yaudarar mutane ta intanet
  • Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 10 Da Aka Yi Garkuwa Da Su Bayan Kashe Ɗan Bindiga A Katsina
  • Tarayyar Turai Ta Yi Maraba Da Tattaunawa Tsakanin IRAN da Amurka Kan Shirinta Na Makamashin Nukliya
  • Iran ba ta amince da Amurka ba, amma za ta gwada su (Araghchi)