Kungiyar gwagwarmayar Falasdinawa ta Hamas ta ce matakin da Isra’ila ta dauka na hana shigar da kayayyakin jin kai da bukatun yau da kullum a zirin Gaza da aka yi wa kawanya ya zama “laifi na yaki da kuma hukuncin gama-gari.”

A cikin wata sanarwa da ta fitar, Hamas ta ce matakin rufewar ya saba yarjejeniyar tsagaita bude wuta ta watan Janairu ne.

“Irin wannan matakin keta dokokin kasa da kasa da na jin kai, da yarjejeniyar Geneva, kuma laifukan yaki ne da hukuncin gama-gari da ke barazana ga rayukan fararen hula wadanda basu ji basu gani ba.”

Hamas ta ce rufewa da kuma hana shigar da kayan agaji sama da kwana 10 a jere yana kara tsananta radadin da Falasdinawa sama da miliyan biyu ke fama da su, kuma yana nuna yiwuwar fuskantar yunwa a Gaza.

“hana shigar da abinci, magunguna, man fetur, da hanyoyin agaji na yau da kullun ya haifar da tashin gwauron zabin abinci da kuma tsananin karancin magunguna, lamarin da ya ta’azzara matsalar jin kai a Gaza.”

Hamas ta yi kira ga masu shiga tsakani da su matsa wa gwamnatin kasar lamba wajen “cika alkawurran da ta dauka” a karkashin yarjejeniyar tsagaita bude wuta.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: hana shigar da

এছাড়াও পড়ুন:

Hamas : tattaunawa ce kawai mafita ta sakin wadanda ake garkuwa dasu

Kungiyar gwagwarmayar Falasdinawa ta Hamas ta yi imanin cewa barazanar da Isra’ila ke yi na sake dawo da yaki a zirin Gaza ba ta da amfani, tana mai cewa tattaunawar tsagaita bude wuta ce hanya daya tilo da Isra’ila za ta iya ceto rayukan ‘yan kasarta da take garkuwa

ranar Litinin 10 ga watan Maris, kungiyar ta ce Firaministan Isra’ila Benyamin Netanyahu na kawo cikas ga aiwatar da yarjejeniyar saboda wasu dalilai na rajin kansa da kuma na siyasa kawai.

Hamas ta kuma kara jaddada aniyar ta na aiwatar da yarjejeniyar, inda ta bayyana aniyar ta na kaddamar da shirin tsagaita wuta a mataki na biyu ba tare da bata lokaci ba.

Har ila yau kungiyar ta ce gwamnatin Isra’ila tana ci gaba da karya yarjejeniyar tare da kin shiga mataki na biyu, tana mai cewa wannan “jinkirin” ya kara mayar da ita saniyar ware a duniya.

Hamas ta jaddada cewa, masu shiga tsakani na kasa da kasa ne suka yi shawarwari da ita, kuma kasashen duniya sun amince da ita, don haka ta jaddada bukatar tabbatar da aiwatar da ita yadda ya kamata daga gwamnatin kasar don tabbatar da sako mutanen da ta kama.

Tun da farko kakakin kungiyar Hamas Abdul Latif al-Qanou ya bayyana sassaucin da kungiyar ta nuna a lokacin tattaunawar baya-bayan nan da masu shiga tsakani na Masar da Qatar, da kuma wakilin shugaban Amurka Donald Trump a birnin Doha, ya kuma jaddada fatansu na cimma nasarar kammala wannan shawarwarin da Isra’ila.

Ya kara da cewa tattaunawar ta Doha ta shafi kawo karshen yakin, janyewar Isra’ila da sake gina yankin Zirin Gaza.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Fiye da Falasdinawa 130 ne Isra’ila ta kashe tun bayan da aka cimma yarjejeniyar tsagaita wuta
  • Yemen zata sake kai hare-hare kan jiragen ruwan Isra’ila
  • UNRWA ta bukaci Isra’ila da ta bari a shigar da kayan agaji a Gaza
  • Hamas : tattaunawa ce kawai mafita ta sakin wadanda ake garkuwa dasu
  • MDD, ta la’anci Isra’ila kan katse wutar lantarki a Gaza
  • Iran ta soki matakin Amurka na hana shigar da wutar lantarki Iraki
  • Isra’ila ta aike da tawaga zuwa Doha domin ci gaba da tattaunawar sulhun Gaza
  • Isra’ila ta katse wutar lantarki a zirin Gaza
  • New York Times: Isra’ila ce ta kashe wasu fursunoninta da ake tsare da su a Gaza