Aminiya:
2025-04-12@07:30:06 GMT

Matashin da ke kera jiragen sama da bindigogi daga robobi

Published: 12th, March 2025 GMT

Malam Yunusa Alfazazi, dan kimanin shekara 35 kuma mazaunin Kafanchan da ke Karamar Hukumar Jema’a ta Jihar Kaduna, ya kafa tarihi a duniyar fasaha da kirkire-kirkire, inda yake kera jiragen sama da bindigogi da sauran na’urori daga robobi da filastik.

Allah Ya albarkaci Nijeriya da mutane masu fasaha da baiwar kera kayayyaki ba tare da samun horo na musamman ba.

Misali, Malam Yahaya Makera da ya kafa tashar rediyo mai aiki a Kaduna da kayan aikin daba su taka kara sun karya ba.

’Yan bindiga sun yi garkuwa da fasinjoji 450 a Pakistan DAGA LARABA: Asalin Tashe Da Tarihinsa A Ƙasar Hausa?

Haka nan, Mansur Nuhu Bamalli ya samu nasarori a fannin injiniyanci duk da karancin kayan aiki da suke fama da shi da kuma rashin goyon baya na musamman.

Malam Yunusa Alfazazi na daga cikin irin wadannan matasan masu hazaka, wadanda za su iya taka muhimmiyar rawa wajen c-gaban fasaha da kirkirekirkire a Nijeriya idan suka samu goyon baya da tallafin da ya dace.

Duk da irin basirarsa, Yunusa Alfazazi ba injiniya ba ne kuma bai taba halartar wata makarantar koyon fasaha ba.

Kai! Bai ma taba halartar wata makarantar zamani ba. Da kansa ya koyar da kansa, ya kuma ci gaba da inganta fasahar tasa a tsawon shekaru ta hanyar gwaje-gwaje da bincike.

Duk da wannan basirar tasa, matasyin yana sana’ar tura baro ne da yin dako wajen samun na rufin asiri, duk da kasancewarsa bai taba aure ba.

Gwamna da Babban Hafsan Tsaro sun yaba masa

Ayyukan Yunusa ba na wasa ba ne, domin yana kera samfurori masu cike da tsari da fasaha, wadanda suka ja hankalin manyan mutane, ciki har da Babban Hafsan Tsaron Nijeriya, Janar Christopher Gwabin Musa, da tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir Ahmad El-Rufai.

A wata ziyara da El-Rufai ya kai garin Kafanchan, ya yi mamakin fasahar Yunusa.

“Gwamna El-Rufai ya tambaye ni ko ni ne na kera jirgin saman da ya gani. Na amsa masa da eh, sai ya ba ni katin tuntubarsa domin mu yi magana kuma na ba shi kyautar helikwaftar.

“ Amma gaskiya ban kira shi ba. Wannan abin ya faru ne lokacin yana gwamna,” in ji Yunusa.

Haka nan, Janar Christopher Gwabin Musa ya yaba da fasahar matashin, tare da sayen daya daga cikin bindigogin roba da ya kera.

“Ya yaba min, ya ba ni kyauta, kuma ya karbi bindigar,” in ji Yunusa, wanda ya ce “ban samu horo na musamman a kan aikin ba.”

Ya dai dogara ne da kokarinsa da baiwarsa kawai tare da lura da yanayin abuguwan.

Ya ce, “Na fara ne da kera kananan motocin roba da bindigogi. Daga baya kuma sai na fara kera jiragen sama.”

Hazakarsa tasa ta kunsshi sarrafa abubuwa daga kayayyakin da aka yi watsi da su zuwa abubuwa masu ban mamaki ne.

Yana amfani da robar danko da filastik don kera samfurorin jiragen sama da bindigogi kala-kala da suka yi kama da na gaskiya.

Abin da ya fi burge mutane game da shi shi ne yadda ba ya amfani da na’urorin aiki na zamani.

Da kayan aiki na yau da kullum da kuma kwarewarsa yake kera kayayyaki masu tsari kamar na gaske.

Jiragensa na sama, ko da yake kanana ne, suna da bangarori masu motsi da ke yin aiki kamar na gaske.

Bindigoginsa kuwa da ya kera daga robobi da filastik, suna daukar hankali, kai ka ce bindigogi ne na gaskiya.

Zan iya fiye da wadannan —Alfzazi

Sai dai duk da kwarewarsa, Yunusa bai samu wata dama da za ta amfane shi ba har zuwa yanzu.

Wannan shi ne irin yanayin da wasu matasan Nijeriya ke fuskanta ta shi na rashin jagoranci ko tallafi daga gwamnati ko kungiyoyi masu zaman kansu, lamarin da ya haifar wa da tafiyar Yunusa cikas da kalubale.

Babban burinsa shi ne gwamnati ta dauke shi aiki a wata hukuma da ke kula da kera kayayyaki irin wadannan domin ya ba da tasa gudunmawarsa ga ci-gaban kasa.

Ya ce, “Ina jin zan iya yin fiye da abin da nake yi idan aka ba ni dama. Ina so in zama wani bangare na wani gagarumin aiki domin in taimaka wajen kera kayayyakin da za su amfanar da Nijeriya.”

Rashin tallafi

Amma saboda rashin goyon baya, yana dogaro ne da dan abin da da yake samu daga mutanen da ke sha’awar ayyukansa.

Wani lokaci kuma yana tura baro ne don yin dako domin ya samu abin da zai ci.

“Ba ni da iyali, kuma ba ni da aiki. Nakan samu wasu ’yan kudi ne daga mutanen da ke sha’awar aikina.

“Wasu lokutan kuma sai na yi dako ta hanyar tura baro nake samun abin dogaro a rayuwata. Wannan ne yake ci gaba da karfafa min gwiwa.”

‘Jami’in tsaro ya sa ni a tsaka-maiwuya’

Duk da girmamawar da yake samu, yana kuma fuskantar gargadi daga jami’an tsaro.

Ya ce, “Wani jami’in tsaro ya taba gargadina cewa in kula da kyau kada in rika yada sirrin fasahata ga mutanen da ba su dace ba.

Ya ce in kiyaye sosai kada in sayar da fasahata ga kowa.”

Matashin ya ce, wannan gargadin ya kara jefa shi cikin damuwa da rashin tabbas game da inda zai dosa yanzu da irin wannan fasahar kuma da suwa zai yi hulda har ta kai shi ga samun hadin gwiwa da mutanen da za su iya taimaka masa.

Duk da cewa yana fahimtar tasirin sirri da tsaro da ke tattare da aikinsa, amma yana gudun kada ganin baiwarsa ta tafi a banza.

 “Idan da zan samu damar yin aiki tare da hukumomin gwamnati ko masana’antu masu zaman kansu, zan iya amfani da baiwata ta hanyoyin da za su amfanar da kasa,” in ji shi.

Yadda za a ci moriyar basirar

Nijeriya tana fama da matsalar yawan kaurar masu basira zuwa kasashen waje, ko kuma rashin amfani da baiwar da ake da ita saboda rashin damarmaki.

Lamarin Yunusa misali ne na irin mutane masu hazaka da ke fuskantar kalubale a kasar da ke neman ci-gaban fasaha.

A yayin da ake kokarin kera kayayyakin soja da na tsaro a Nijeriya, ana bukatar matasan irin Yunusa su samu goyon baya, a maimakon barinsu da ake yi su kasance ba su ga tsuntsu ba su ga tarko.

Ya kamata gwamnati da kungiyoyi su fara karkatar da hankalinsu ga irin wadannan mutanen masu basira.

Idan aka ba shi horo da jagoranci, Yunusa zai iya zama kwararre a bangaren fasaha da kirkire-kirkire.

Idan aka ba shi tallafin ilimi, zai iya zurfafa bincike da kirkirar sabbin abubuwa. Idan kuma kamfanoni masu zaman kansu suka tallafa masa, zai samu damar fadada ayyukansa.

Yadda za abunkasa basirarsa

“Baya ga tallafin kudi, abin da Malam Yunusa ke bukata shi ne haduwa da kwararru a fannin injiniyanci da za su jagorance shi kan hanyoyin da suka dace.

Ta hakan, zai iya fahimtar fasaha yadda ya kamata kuma ya kera kayayyakin da za a iya fitarwa kasuwanni.

“In har aka kula da shi yadda ya kamata, na iya zama wani babbar dama ga Nijeriya a bangaren kere-kere.

“Zai iya zama jagora a fasahar kera jiragen sama da kayayyakin tsaro,” a cewar Malam Auwal Ibrahim Shehu, Daraktan kungiyar Haske Peace Debelopment Initiatibe, wata kungiya mai zaman kanta da ke Kaduna.

Malam Yunusa ya bayyana cewa yana da kwarin gwiwa a kan baiwarsa, duk da matsalolin da yake fuskanta.

Yunusa ya ce, “Na san ina da wata baiwa mai amfani. Abin da kawai nake bukata shi ne dama domin in nuna duniya abin da zan iya yi.”

Ko labarinsa zai zama nasara a gare shi da kasar gaba daya, ko kuma baiwarsa zata watse, hakan ya dogara ne da yadda Nijeriya za ta dauki mataki a kan lamarinsa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: kera jiragen sama jiragen sama da

এছাড়াও পড়ুন:

Waraka Daga Bashin Ketare

 

Amfanuwa Da Mamakon Arziki Da A Ka Yi Mana Baiwarsu

Babu shakka, mutuwar zuciya ce ta mai da jama’ar wannan Kasa tamu ta Nijeriya dogara kacokan da sabgar man fetur, a matsayin wata hanya daya tilo da za ta rika samar mana da sama da kashi tamanin ga tattalin arzikinmu na Kasa!. Hakika akwai hanyoyin arzuka iri daban daban cikin wannan Kasa, wadanda ma suka kere fetur sau ninkin ba ninki wajen bunkasar sha’anin tattalin arziki, musamnan sabgar noma, wadda wasu Shekaru can baya, ita ce kashin bayan tattalin arzikin wannan Kasa. Kuma, tun daga wancan lokaci zuwa yau din, harkar noma ce kan gaban fetur, wajen samawa dubban jama’ar Kasa aiyukan-yi.

Yankin arewacin wannan Kasa ta Nijeriya, na daga wuraren da suka fi ko’ina a Duniya kyawon kasar noma. Yankin na arewa, ya fi ko’ina a yankin Afurka ta yamma (West Africa) yawan matattarar ruwa, ko a ce dam dam, wanda ake amfani da su wajen noman rani. Ga dandazon albarkar jama’a da Allah Ya ba mu, wadanda za su wadata wajen noma irin wadannan kyawawan kassai da aka yi mana baiwarsu. Bangaren noman ne ke samawa dubban jama’ar yankin aiyukan-yi sama da komai a ban Kasa, sai dai, shugabanni sun gaza shigowa bangaren na noma, don inganta shi ingantawa.

A Kasar Amurka, Kasar da shugabanni suka shiga harkar tallafar noma kan-jiki kan karfi, ta tabbata cewa, kudin shigar da lemon zaki “Orange” kawai ke samawa Kasar a Shekara, ya fi kudin shigar da gwamnatin Nijeriya ke samu a Shekara wajen man fetur!. Ita kanta Amurkar, ba za ta fada mana ni’imar albarkatun kasa ba, amma sai ga su sun fi mu amfanarsu. Me ya sa? Amsa, shugabanninsu da gaske ne suke, a yunkurinsu na inganta tattalin arzikin Kasar.

Iskar gas kawai da Allah Yai wa Nijeriya baiwarsa, zai iya daukar nauyin bai wa daukacin nahiyar Afurka da ke kunshe da Kasashe 52 ko 53 wajen sama musu wadatacciyar iskar gas. To Amma dan Nijeriya a yau, nawa ne yake shan litar gas? Da kuma mai karatu zai lalubi wasu Kasashe cikin Duniya da ko kama kafarmu ba su yi ba wajen mallakar iskar gas din, sai ya samu kuma sun fi mu shan gas din da arha!. Wadanne irin shugabanni muke da su ne? Eh mana, tun da sarrafawa da inganta harkar gas din, na hannunsu ne.

Misali mutum ya ce fetur, gas, rake, lemo da makamantansu, za a ga an ba mu albarkatun kasa na abubuwa daidai har sama dari biyu da hamsin (250) iri daban daban. Cikin wadannan albarkatun kasa akwai bishiyar Katako, wani masani ke cewa, da Nijeriya za ta inganta bishiyoyin Katako da take da su, su kadai, za su iya zama abin dogara kamar man fetur, kuma su rike Kasar. Wane shiri ne a kasa a yau da mutanen wannan Kasa za su ce sun ga gwamnati na yi, don inganta sabgar bishiyoyin Katakonta?

Mutum ya dauki gyada kawai, zai yi matukar mamakin irin tattalin arzikin da ke kunshe cikinta. Daga gyada, akwai sinadaran da ake yin sabulu, abin yin biskit, abin yin abincin dabbobi, abincin kifi, abincin kaji da sauransu. Ka da mai karatu ya mance da man girki da ake samu daga gyadar. Ko mai karatu ya san da cewa a na yin makarin inji daga matsanancin hucin zafi, wanda a turance ake kira da “engine gasket” da bawon gyadar? To amma a yau, wane hobasa ne na hakika ba na baka ba, da za a ce gwamnatocinmu na yi, don ganin mun amfana hakikar amfanuwa daga mamakon tattalin arziki da ke kunshe cikin gyada?

Cikin wata budaddiyar wasika da Dattijo, Alhaji Dattijo Adhama ya rubuta zuwa ga hukumomi masu gudanarwa da masu yin doka na arewacin wannan kasar, “An Open Letter To The Northan Edecutibes & Legislatures” a Watan Yulin Shekarar 2021 (July, 2021), da mutum zai duba shafi na biyar (P5) na wannan wasika, zai amfana da wata irin kididdiga da aka yi, wadda ta nuna irin biliyoyin kudaden da jihar Kano za ta iya samu a kullum daga man gyadar da za a sha a cikin jihar. Cikin kididdigar, an nuna cewa, jihar ta Kano na iya samun kudin shiga sama da naira biliyan saba’in da biyu (N72b) a kullum. Da sharadin, wancan bangare na masu zartarwa da masu doka sun shigo sun gama kai wajeguda, tare da datse shigowar man gyadar daga Kasashen ketare, ta hanyar yin doka a Majalisa.

A tsakanin garin Makoda da Dambatta, akwai wani nau’in yashi da Kasar China ke ta begen ganin ta sami kai wa ga tononsa, don sana’anta gilashi da shi. Duk cikar Kasar ta China, ba su da wani ma’adin yin gilashi sama da irin wannan yashi na tsakanin Dambatta da Makoda. Idan ban manta ba, wani lokaci can baya, ta hanyar Malam Gambo, shugaban ma’aikata “Staff Officer” na Kasuwar Sabon Gari, ya gabatar min da shugabancin masu harkar gilashi ta Kasuwar Kofar Ruwa, na wuce gaba zuwa kai kuka ga Sanatan yankin, Barau Jibril”, da zimmar ya wuce musu gaba wajen tono yashin, amma lamarin ya gagari kundila.

Ba sai Kano ba, muddin mai karatu dan Nijeriya ne, ba zai gaza tunanin wani ma’adin ko albarkar Kasa da Allah Ya hore musu a yankinsu ba. Babbar matsalar a yau ita ce, masu mulki ba su damu da hako ko amfanar da jama’ar Kasa daga irin wadancan amfanoni da Allah Yai mana baiwarsu ba. Sai ma aka wayigari, idan akwai wani ma’adani a waje, sai a sami wasu marasa kishin kasa su game baki da Turawa, a zo a haddasa mummunar fitinar da za ta kai ga kashe rayukan dubban jama’a a wajen. Bayan kowa ya yi kaura ya yi gudun tsira da ransa, sai wadancan marasa kishin kasa da bakin haure su dukufa kwasar wadancan ma’adanai, shin, me ke faruwa a Zamfara a yau?

Duk irin albarkatun kasa da aka yi wa wata Kasa baiwarsa a Duniya, muddin shugabanninta ba sa kishinta, to fa a banza, ba za su amfana ba. Kuma ba za a bar su su zauna lafiya ba.

Da shugabanni a Nijeriya za su karkata ga sabgar noma kadai, su zuba jari ciki, su samawa manoman taki da kasuwa, babu shakka da an fita daga wannan kagaggen talaucin da aka jefa jama’ar wannan Kasa ciki. Talaucin Kasar Nijeriya ba daga ne yake ba, tun da Allahn Ya ba da mafita.

 

Samar Da Gungun Masana Masu Kishin Kasa

Dole ne gwamnati ta yi zabarin manyan mutane masana gogaggu, wadanda lamarin Kasar ne ke kunshe cikin zukatansu sabanin muradansu na son zuciya. Hakika Allah Yai mana baiwar mutane hazikai masana, wadanda hatta sassan Kasashen Duniya ke daukarsu aikin dindindin da na kwantaragi, don inganta harkokin Kasashen nasu. Dole ne a lalube su, a saurari shawarwarinsu, a dabbaka abubuwan da za su gabatar a matsayin shawara ko a matsayin wani sharadin da wajibi ne binsa, wajen inganta harkokin tattalin arzikin namu, muddin a na son A’i ta fita daga rogo ba tare da ta karce jiki ba.

Lokacin da marigayi Umar Musa ‘yar’adua ya tasamma yin gyara game da sha’anin Zabe a Nijeriya, ya kafa wani babban Kwamiti ne a karkashin tsohon babban Joji na Kasa Uwaisu, da sauran masu kishin kasa, mutane irinsu Farfesa Attahiru Muhammad Jega, OFR, ai sanin kowane cewa, a karshe, laya ta yi kyawon rufi. Gwamnati ba ta yi wa kwamitin wani katsa-landan ba, sannan kuma ta tasamma dabbaka irin shawarwarin da wancan kwamitin ya gabatar mata. Bugu da kari, gwamnati ta dauko guda daga cikin ‘yan kwamitin, Jega, ta danka hukumar zaben Kasar kacokan a hannunsa, hakan ne ya jaza aiwatar da zabukan da ba a taba samun masu ingancinsu ba cikin tarihin Zabukan Kasar gabaninsu, wato Zabukan Shekarun 2011 da na 2015, kamar yadda masana da sauran masu sanya idanu na gida da waje suka fadi.

Ko da an kafa wani kwamiti na masana kuma masu kishin kasar, muddin za a yi musu katsa-landan cikin sabgar kwamitin, ko kuwa, shawarwarin da suka gabatar, a yi wurgi da su, to fa babu inda za a je, sai dai kawai a ci gaba ne da tsalle a wajeguda kamar yadda aka saba.

Duk kyawon wani kwamiti da sunan gyara tattalin arzikin Kasa da aka kafa, ko za a kafa ba bisa cikakkiyar cancanta ba, shi ma ba zai cimma komai ba mai alfanu, lamura za su ci gaba da wakana ne cikin yanayi na daben-kwalo.

Duk karatu da Dr Abel Guobadia da Professor Maurice Iwu ke da, ba su jagorantar Hukumar Zabe, INEC, ta Kasa da aka yi bisa wata manufa, a karshen lamarin, sun gudanar da wasu nau’ikan Zabuka ne gurbatattu, wadanda gabaninsu a Kasar, ba a taba cin karo da miyagun Zabukan irinsu ba!.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • 2027: Masu Shirin Yin Kawance Na Duba Yiwuwar Zakulo Dan Takarar Da Zai Yi Wa’adi Daya
  • Darasi daga rayuwar Dakta Idris AbdulAzeez Dutsen Tanshi
  • Waraka Daga Bashin Ketare
  • Shugaban Kasar Amurka Yace Yana Kokarin cimma yarjeniya da kasar China Dangane da Tiktok
  • Sojojin Sama Na HKI Kimani 1000 Guda New Suka Bukaci A Kawo Karshen Yaki A Gaza
  • Yadda Tinubu ya taimaka wa ’yata ta samu aiki a NUPRC — Buba Galadima
  • Yadda Tinubu ya taimaka wa ’yata ta samu aiki NUPRC — Buba Galadima
  • Malaman Makarantun Firamare 1,800 Sun Samu Horo Aka A Kwara
  • Jiragen Yaki Da Sojojin Kasa Na HKI Sun Kashe Falasdinawa 38 A Yankin Gaza Daga Safiyar Yau Zuwa Yanzu
  • Rahoto : Amurka za ta iya janye sojoji 10,000 daga Tsakiyar Turai