Cutar Sanƙarau Ta Kashe Mutum 26, 248 Sun Kamu A Kebbi
Published: 12th, March 2025 GMT
Alamomin cutar sun haɗa da ciwon kai mai tsanani, ciwon wuya, tari, da amai.
Yaɗuwar cutar a Kebbi na iya shafar sauran jihohin da ke maƙwabtaka da ita, musamman Zamfara, Sakkwato, da Neja, inda ake yawan tafiye-tafiye tsakanin jihohin.
Hakan na nuni da buƙatar gaggauta ɗaukar matakan kariya don hana cutar yaɗuwa zuwa sauran yankuna.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Sanƙarau
এছাড়াও পড়ুন:
Jihohi 12 da za a fuskanci tsananin zafin rana — NiMet
Hukumar kula da yanayi ta Nijeriya NiMet ta yi gargaɗin cewa akwai yiwuwar a fuskanci tsananin zafin rana a wasu jihohin ƙasar na tsawon kwanaki huɗu.
Wata sanarwa da Nimet ta fitar ranar Litinin a Abuja, ta ce mutane su guji fita cikin tsananin zafi musamman daga karfe 12 na rana zuwa karfe 3.
Ainihin abin da ke kawo wa Manchester United koma baya ‘Yarjejeniyar sayar wa Matatar Dangote ɗanyen mai a farashin naira za ta ƙare a ƙarshen Maris’Hukumar ta ce mutane za su ji sauyin al’amura a tsawon lokacin da za a kwashe ana tsala zafin ranar.
Jihohin da aka yi hasashen za su fuskanci ƙaruwar yanayi na zafin rana sun haɗa da Neja da Kwara da Oyo da Kogi da Nasarawa da kuma Benue.
Sauran sun haɗa da Enugu da Anambra da Abia da Ebonyi da Cross River da birnin tarayya Abuja.
NiMet ta ce wasu jihohin da ka iya fuskantar wannan barazana sun hada da Taraba da Adamawa da Filato da Kaduna da Zamfara da kuma Sakkwato.
Ta kuma shawarci al’umma da su riƙa shan isasshen ruwa a tsawon lokacin – su kuma yi amfani da fanka da na’urar sanyaya ɗaki da kuma zama a wurare masu inuwa.