Kungiyar Tarayyar Turai ta yi barazanar sake kakaba wa Syria takunkumi
Published: 12th, March 2025 GMT
Jami’ar kula da manufofin ketare ta Tarayyar Turai, Kaya Kalas, ta tabbatar da cewa, EU za ta iya sake kakaba takunkumi kan kasar Syria, idan aka samu tabarbarewar lamurra, tana mai nuni da yadda ake cin zarafin fararen hula a gabar tekun Syria.
Kaya Kalas ta shaidawa kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya cewa, “Muna shirye-shiryen mayar da takunkumi kan Syria, idan muka ga tabarbarewar lamurra na ci gaba, inda ta jaddada cewa, dole ne mika mulki ya kasance cikin lumana da kuma hadin kai, kuma dole ne a kare fararen hula a kowane hali.
Ta bukaci dukkan masu ruwa da tsaki na waje da su mutunta hadin kan Syria, da kuma iko da iyakokinta.”
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Tawagogin gwamnatin Kongo da kungiyar M23 sun isa Doha domin tattaunawa
Jami’an Kongo da masu shiga tsakani na M23 sun isa Qatar domin tattaunawa don cimma yarjejeniyar tsagaita wuta.
Jami’an Kongo da masu shiga tsakani na kungiyar M23 sun isa Doha babban birnin kasar Qatar domin tattaunawa da nufin cimma tsagaita bude wuta da kuma kawo karshen fadan da aka shafe watanni ana gwabzawa a yankin, kamar yadda wasu majiyoyi hudu suka shaida wa kamfanin dillancin labarai na Reuters a jiya Alhamis.
Wakilan tawagogin biyu sun tabbatar da kasancewarsu a babban birnin kasar Qatar, kuma sun ce za a yi ganawar ido-da-ido a ranar Laraba, amma har yanzu suna tattaunawa kan tsarin tattaunawar.
Dukkanin majiyoyi – jami’an gwamnati biyu da wakilan ‘yan tawaye – sun bukaci a sakaya sunansu saboda masu shiga tsakani na Qatar sun nemi kada su yi magana da manema labarai.
Qatar ta yi wata ganawa a watan da ya gabata tsakanin shugaban kasar Congo Felix Tshisekedi da takwaransa na Rwanda Paul Kagame. Wannan ita ce ganawa ta farko da shugabannin biyu suka yi tun bayan da kungiyar ta kaddamar da hari a ranar 23 ga watan Maris din da ya gabata. Yunkurin yin shawarwarin zaman lafiya na baya-bayan nan shi ne yunkurin kawo karshen rikicin da aka kwashe shekaru ana yi, wanda ya samo asali daga kisan kiyashin da aka yi a kasar Rwanda a shekara ta 1994.
Wata majiya da ke da masaniya kan shiga tsakani na Qatar ta shaidawa kamfanin dillacin labarai na Reuters cewa bangarorin biyu sun yi wata ganawar sirri a birnin Doha a farkon wannan wata domin shirya tattaunawar sulhu. Sai dai har yanzu tattaunawar da aka shirya fara a ranar Laraba na fuskantar cikas.