Aminiya:
2025-04-12@04:26:44 GMT

Ukraine ta amince da kudurin tsagaita wuta a fafatawarta da Rasha

Published: 12th, March 2025 GMT

Ukraine ta amince da kudurin tsagaita wuta na wata guda a yaƙin da ta shafe shekaru uku tana fafatawa da kasar Rasha.

Matakin na zuwa ne bayan tattaunawar da wakilan ƙasar ke ci gaba da yi yanzu haka da Amurka a birnin Jedda na Saudiya.

Matashin da ke ƙera jiragen sama da bindigogi daga robobi Rikicin ƙabilanci ya yi ajalin mai juna biyu da wasu mutum 10 a Nasarawa

Sakataren Harkokin Wajen Amurka, Marco Rubio ne ya sanar da haka da maraicen Talata bayan shafe wuni guda jami’an Ukraine da na Amurka suna tattaunawa don samar da zaman lafiya tsakanin Ukraine din da Rasha.

Rubio ya ce makasudin gabatar da kudurin shi ne na dakatar da bude wuta da kashe mata da kuma kananan yara a Ukraine.

Sakataren ya kuma kara da cewa a yanzu zabi ya rage ga Rasha na ta amince da kudurin ko kuma akasin hakan.

Sakataren ya kuma kara da cewa a yanzu zabi ya rage wa Rasha, inda kowanne lokaci daga yanzu ne ake shirin miƙa mata ƙunshin matsayar da aka cimma a wannan taro na Jedda don nazartarta da kuma yiwuwar aminta da ita ko akasin haka.

Wasu majiyoyi sun bayyana yiwuwar Donald Trump ya tattauna da Vladimir Putin a cikin makon nan bayan matakin na Ukraine dangane da amincewa da tayin Washington kan tsagaita wuta a yaƙin ɓangarorin biyu.

Har ila yau, Amurkar ta kuma amince ta koma bai wa Ukraine din bayanan sirri da kuma tallafin tsaro.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Rasha Saudiyya Ukraine

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Kasar Iran Ya Ce Iran Ba Zata Jada Bayan Ba A Kan Shirinta Na Makamashin Nukliya

Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkiyan ya bayyana cewa JMI ba zata taba jada baya a kan shirinta na makamashin Nukliya ba, kuma yayi allawadai da duka wani shiri na kaiwa cibiyoyin nukliyar kasar Hare-hare.

Tashar talabijin ta Presstv ta nakalto shugaban yana fadar haka a taron raya ranar Nukliya ta karo karo na 19 a wanda aka gudanar a nan Tehran.

Shugaban ya kara da cewa, Iran bata neman yaki da kowa, amma zata maida martani kan duk wata takala daga HKI ko Amurka. Ya ce Iran ba zata amince wani ya hana mutanen kasar amfani da fasahar da All..ya hore masu ba. Ya kuma kara jaddada cewa JMI bata neman mallakar makaman Nukliya.

A rana irin ta yau ce wato 9 ga watan Afrilun shekara ta 2006, masana fasahar nukliya na JMI suka sami nasara a karon farko suka samar da makamashi daga fasahar nukliya tare da amfani da sinadarin Uranium.

A yau shekaru 19 kenan tun lokacin kasar take samun ci gaba a fasahar Nukliya da kuma amfaninsa. Inda ya ma kasar ta kaddamarda sabbin ci gaban da ta samu tare da amfani da makamacin Nukliya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Har Yanzu Shugabanci NNPP Na Hannunmu – Tsagin Kwankwaso
  • Mai Martaba Sarkin Kano 16 Ya Nada Mannir A Matsayin Sabon Galadiman Kano
  • Sharhin Bayan Labarai: Yakin Kasuwanci Tsakanin Amurka da Kasashen Duniya
  • Mutanen da suka saba ba ni abinci yanzu na neman taimako — Obi
  • Shugaban Kasar Iran Ya Ce Iran Ba Zata Jada Bayan Ba A Kan Shirinta Na Makamashin Nukliya
  • Iran ba ta amince da Amurka ba, amma za ta gwada su (Araghchi)
  • Majalissar Dokokin Rasha ta amince da yerjejeniyar huldar ta shekara 20 da Iran
  • Rahoto : Amurka za ta iya janye sojoji 10,000 daga Tsakiyar Turai
  • Ibas ya naɗa kantomomin ƙananan hukumomin Ribas
  • Iran: Tattaunawa kai tsaye da Amurka a yanzu ba shi ne zabinmu ba