Aminiya:
2025-03-12@18:04:57 GMT

Dan ta’adda zai biya tarar miliyoyi bayan shan dukan kawo wuka a Katsina

Published: 12th, March 2025 GMT

Wani dan bindiga da ya karya yarjejeniyar sulhu a Karamar Hukumar Jibiya ta Jihar Katsina mai suna Bala Wuta na Garin Mazanya, na can kwance rai-kwakwai-mutu-kwakwai bayan ya sha dukan kawo wuka.

Tubabbun ’yan bindiga sun yi wa Bala wuta takakkiya ne har gida inda suka yi masa bugun dawa, bayan da ya yi garkuwa da wasu matafiya jim kadan bayan sulhun da aka yi, inda bayan sun lugwiwita shi, suka wajabta masa biyan tarar Naira miliyan uku.

HOTUNA: Fashewar tankar gas ta kashe gomman mutane a Legas HOTUNA: An hana Gwamna Fubara shiga Majalisar Dokokin Ribas

Ana iya tuna cewa, a ranar 28 ga watan Fabrairu, 2025 ne aka yi sulhun, wanda ya samu wakilcin sojoji da ’yan sanda da sauran jami’an tsaro da masu ruwa karkashin jagorancin shugaban karamar hukumar ta Jibiya Alhaji Maitan, kamar yadda su ’yan bindigar suka nema.

’Yan bindigar da suka halarci zaman a karkashin jagoransu Audu Lankai, sun hada da Kantoma da Ori da Tukur Dan Najeriya da Bammi da sauransu da suka fito daga yankin Zamfara.

Yarjejeniyar da aka kulla

Jama’ar yankin sun shimfida wa ’yan bindiga sharadin barin kai hare-hare a fadin karamar hukumar da hanyar Katsina zuwa Jibiya da hanyar Jibiya zuwa Gurbi da kuma wadda ke zuwa Batsari.

Za kuma su da daina kai hari ko barna a gonaki ko cikin daji ko guje-guje a kan babura a cikin garin ko nuna rashin da’a ko tarbiyya ga al’umma.

Kazalika, yarjejeniyar ta bukaci za su kiyaye duk dokokin gwamnati su kuma daina yawo da makamai a bainar jama’a.

A nasu bangaren, tubabbun ’yan bindigar dajin sun shardanta a daina kashe su ko kama dabbobinsu babu dalili da kuma tabbatar da adalci a tsakaninsu da sauran al’umma a matsayinsu na ’yan kasa.

Sa’annan sun bukaci a daina daukar doka da hannu a rika barin hukuma ta yi hukunci ga mai laifi.

Bayan nan ne suka sako mutane 10 na garin Daddara da ke hannunsu tare da mika bindiga kirar AK-49 guda biyu.

Bala Wuta ya ji a jikinsa

Sai dai duk da wannan yarjejeniyar sulhu da aka kulla, sai ga shi a ranar Alhamis da ta gabata, wani wanda bai shiga sulhun ba mai suna Bala Wuta na Garin Mazanya da ya addabi hanyar zuwa Jibiya, ya kayar da wata mota ya yi awon gaba da matafiya a Mallamawar Batsari — garin su Lankai.

A dalilin haka shi Audu Lankai jagoran sasanci ya taras da shi har gida ya yi mishi dukan kawo wuka sannan ya sanya masa tarar kudi har naira milyan uku.

Har zuwa yanzu, wakilinmu ya ruwaito cewa, Bala Wuta yana can kwance yana jin jiki a garin na Mazanya.

Labarin da muka samu daga garin na Jibiya an ce, a ranar Lahadi an ga Fulanin da ke cikin dajin sun shigo kasuwa mazansu da matansu cikin murna saboda samun wannan ’yanci.

Majiyarmu ta shaida mana cewa, Fulanin sun rika sayen lemon kwalba mai sunyi da ake sayarwa Naira 250, wanda suke cewa a can daji naira dubu ake sayar musu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jibiya yan bindiga

এছাড়াও পড়ুন:

Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Kano, Sun Sace Mutum Ɗaya

Wasu ‘yan bindiga sun farmaki gidan Alhaji Yusha’u Ma’aruf, mamallakin wani asibiti mai zaman kansa, a garin Zakirai da ke ƙaramar hukumar Gabasawa a jihar Kano, inda suka sace wani matashi mai shekaru 20 tare da jikkata ɗan uwansa.

Rahotanni sun bayyana cewa maharan uku ɗauke da bindigogi da adduna sun afka wa gidan da misalin ƙarfe 2:15 na dare, suka sare yatsan hannun Abubakar Yusha’u mai shekaru 23 sannan suka sace ɗan uwansa, Mohammed Bello Yusha’u.

Daily Trust ta ruwaito cewa, sun kwashe wayoyi da kuɗaɗe kafin su tsere.

Tinubu Ya Buƙaci A Mayar Wa BUK Filin Rimin Zakara Da Ake Taƙaddama A Kai Ɗan Uwan Gwamnan Kano Da Malaman NNPP Sun Koma APC

Kakakin rundunar ‘yansandan Kano, Abdullahi Haruna Kiyawa, ya tabbatar da faruwar lamarin, yana mai cewa jami’an tsaro sun fara bincike don ceto wanda aka sace da kuma kamo waɗanda suka aikata harin.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yansanda Sun Daƙile Yunƙurin Yin Garkuwa Da Mutanen 30 A Katsina
  • ’Yan sanda sun ceto mutum 30 daga hannun ’yan bindiga a Katsina
  • HOTUNA: Fashewar tankar gas ta kashe gomman mutane a Legas
  •  Uganda Ta Aike Da Sojoji Zuwa Sudan Ta Kudun Domin Kare Babban Birnin Kasar
  • Ainihin abin da ke kawo wa Manchester United koma baya
  • ’Yan bindiga sun kashe manoma 14 a Ondo
  • Abin da ya sa na sauya sheƙa daga APC zuwa SDP — El-Rufai
  • ’Yan bindiga sun yi garkuwa da matashi a Kano
  • Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Kano, Sun Sace Mutum Ɗaya