Aminiya:
2025-03-12@20:56:18 GMT

Zulum ya bai wa ƙananan ’yan kasuwa tallafin 1bn a Borno

Published: 12th, March 2025 GMT

Gwamnan Jihar Borno, Babagana Umara Zulum, ya raba wa ƙananan ’yan kasuwa da matsakaita su 9,403 a ƙananan hukumomin Biu da Hawul, tallafin Naira biliyan ɗaya.

Wannan tallafi na da nufin ƙarfafa kasuwanci, haɓaka tattalin arziƙi, da rage talauci a yankunan.

Dan ta’adda zai biya tarar miliyoyi bayan shan dukan kawo wuka a Katsina Ukraine ta amince da ƙudurin tsagaita wuta a fafatawarta da Rasha

A Biu da Hawul, gwamnan ya raba Naira miliyan 560.

3 ga ’yan kasuwa 5,603, inda kowane mutum ya samu Naira 100,000.

Hakazalika, ya raba Naira miliyan 439.7 ga matasa da magidanta 1,800 a Biu da kuma ’yan kasuwa 2,000 a Hawul.

Gwamna Zulum ya ce gwamnatinsa za ta ci gaba da tallafa wa ƙananan ’yan kasuwa da matasa don bunƙasa tattalin arziƙi da samar da ayyukan yi.

Ya buƙaci waɗanda suka samu tallafin da su yi amfani da shi yadda ya kamata, inda ya bayyana cewa hakan na daga cikin alƙawuran da ya ɗauka a lokacin yaƙin neman zaɓe.

Har ila yau, ya umarci hukumar zuba jari ta Jihar Borno (BOSIMP) da ta tantance ƙarin matasa 2,000 marasa galihu domin su ma su amfana da tallafin a nan gaba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yan kasuwa

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yarjejeniyar sayar wa Matatar Dangote ɗanyen mai a farashin naira za ta ƙare a ƙarshen Maris’

Kamfanin Man Fetur na Najeriya NNPC ya ce yarjejeniyar da ya ƙulla da Matatar Dangote domin sayar mata da ɗanyen man fetur a farashin naira za ta ƙare a wannan wata na Maris.

Sai dai kamfanin ce yana tattaunawa da Matatar Dangote domin tsawaita yarjejeniyar sayar mata da ɗanyen mai a naira.

An hana tashe bana a Kano — Nalako NAJERIYA A YAU: Abubuwan Da ke Shirin Faruwa A Fagen Siyasar Najeriya

Sanarwar ta NNPC na zuwa ne bayan wasu rahotonni sun ce kamfanin ya dakatar da sayar wa matatar mai a farashin naira, kamar yadda suka ƙulla yarjejeniya tun da farko.

Wata sanarwa da mai magana da yawun kamfanin Olufemi Soneye ya fitar a ranar Litinin ta ce ba haka lamarin yake, yana mai cewa sai a ƙarshen watan nan na Maris yarjejeniyar za ta ƙare.

“Ya kamata a fahimci cewa yarjejeniyar sayar da ɗanyen mai a farashin naira ta wata shida ce, kuma da sharaɗin akwai man, wadda za ta ƙare a ƙarshen watan Maris na 2025.

“A ƙarƙashin wannan yarjejeniyar mun sayar wa Matatar Dangote gangan miliyan 48 ta ɗanyen man fetur tun daga watan Oktoba na 2024 zuwa yanzu.

“A yanzu muna ci gaba da tattaunawa domin ƙulla wata sabuwar yarjejeniya,” in ji shi.

Masana na cewa idan NNPC ya daina sayar wa Matatar Dangote mai a naira hakan zai iya haddasa hauhawar farashin man, maimakon sauƙin da ake tunanin hakan ya jawo a baya-bayan nan.

Dangote da NNPC sun rage farashi a gidajen mai

A makon jiya ne NNPC ya rage farashin litar man fetur a gidajen mansa da ke faɗin Nijeriya kwanaki bayan matatar man fetur ta Dangote ta rage farashin man a gidajen sayar da mai masu alaƙa da ita.

Ɗaya daga cikin manyan dillalan man fetur a Najeriya ya tabbatar da cewa a yanzu “NNPC na sayar muna da man fetur ne kan naira 840 a Legas, sai kuma naira 875 a Calabar da kuma Fatakwal.”

Hakan na zuwa ne kimanin mako ɗaya bayan Matatar Dangote ta sanar da rage farashin litar man, inda mutanen Nijeriya ke sayen fetur ɗin cikin farashin da ya yi ƙasa da na NNPC a gidajen man da ke haɗin gwiwa da matatar.

Wannan ya sanya aka riƙa ganin dogayen layukan ababen hawa a gidajen man fetur ɗin da ke da alaƙa da matatar ta Dangote.

Farashin da Dangote ya sanar zai riƙa sayar wa dillalai abokan hulɗarsa shi ne naira 825 daga 890, ragin naira 65 ke nan kan kowace lita.

Karo na biyu ke nan kamfanin yana rage farashin man a watan Fabrairun 2025, abin da dillalan man suka bayyana da “abin a yaba.”

Rage farashin ya sa man na Dangote ya zama mafi rahusa idan aka kwatanta da wanda ake shigo da shi ƙasar daga ƙetare.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar wakilai ta dakatar da CBN daga ƙara kuɗin cajin ATM
  • Boko Haram Sun Yi Yunƙurin Afkawa Tawagar Gwamna Zulum
  • Gwamna Buni Ya Naɗa Matasa 200 A Matsayin Hadimansa
  • Gidauniyar Marayu Riyadissalihin ta Funtua Ta Raba Kayayyakin Ramadan
  • ‘Yarjejeniyar sayar wa Matatar Dangote ɗanyen mai a farashin naira za ta ƙare a ƙarshen Maris’
  • Nijeriya Ta Shigo Da Man Fetur Na Naira Tiriliyan 12 A 2024 – Rahoto
  • Tambuwal Ya Tallafawa Magidanta Dubu 30 Da Kayan Abinci
  • Sojoji Sun Miƙawa Gwamnatin Borno Mutane 75 Da Suka Ceto