Da jijjifin safiyar yau Laraba ne aka harba rukunin taurarin dan’adam masu karamin zango daga doron kasa guda 18 a cikin roka kirar Long March-8 Y6, daga cibiyar harba kumbo ta kasuwanci ta lardin Hainan da ke kudancin kasar Sin.

Taurarin na dan’adam da aka harba, wanda rukuninsu shi ne na biyar a cikin nau’o’insa, sun shiga falakin da ake so cikin nasara, kamar yadda hukumar kula da kimiyya da fasahar sararin sama ta kasar Sin (CASC) ta bayyana.

Hukumar ta kara da cewa, taurarin za su kasance rukunin taurarin dan’adam na kaddamar da ayyukan intanet na kasuwanci na kasar Sin.

Wannan aiki na bincike da aka kaddamar na farko daga sashe mai lamba ta 1 na tashar harba kumbon, bayan wanda aka kaddamar a sashen tashar mai lamba ta 2, a ranar 30 ga watan Nuwamban 2024, ya nuna yadda aka kimtsa tsaf a tagwayen shirye-shiryen da tashar sararin samaniya ta farko ta kasuwanci ta kasar Sin ke yi domin gudanar da ayyuka na gaba. (Mai Fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere)

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Masarautar Kauru Ta Bayyana Rashin Sha’awarta Kan Shiga Sabuwar Jihar Gurara

Wata kungiya mai zaman kanta da ke dauke da sunan Kauru Emirate Consultative Initiative (KECI) ta nisanta da yunkurin da wasu ke yi na saka Masarautar Kauru cikin sabon tsarin Jihar Gurara da ake kokarin kirkira daga Jihar Kaduna.

Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Shugaban kungiyar, Malam Isah Mukhtar, ya sanya wa hannu, kuma aka raba wa ‘yan jarida a Zariya.

A cewar Malam Mukhtar, ikirarin da wasu ke yi musamman daga yankin Kudancin Kaduna na cewa Masarautar Kauru na son shiga cikin Jihar Gurara ba gaskiya ba ne kuma yana bata suna.

“Mutanen Masarautar Kauru ba su da hannu a wannan yunkuri. Muna alfahari da kasancewarmu a cikin Jihar Kaduna, musamman saboda alakar tarihi, al’adu da zamantakewa da muke da ita da Masarautar Zazzau,” in ji shi.

Ya ci gaba da bayyana cewa Masarautar Kauru da Masarautar Zazzau na da alaka mai karfi ta fuskar kima da dabi’u da aka gada tun zamanin da.

Yayin da yake karin bayani kan dangantakar zamantakewa da ta tarihi, Malam Mukhtar ya bayyana cewa:

“Daga auratayya, zuwa hanyoyin kasuwanci, bukukuwa da tsarin shugabanci na gargajiya, dukkanmu muna da zumunci da mu’amala da jama’ar Zazzau. Kokarin cire mu daga wannan tsari da saka mu a wani sabon tsari ba zai haifar da alheri ba.”

Ya jaddada cewa Masarautar Kauru “ta yanke shawara a fili” cewa tana so ta ci gaba da kasancewa a cikin sabon tsarin Jihar Kaduna da ake shirin kafawa, tare da kin amincewa da duk wani yunkuri na saka ta cikin Jihar Gurara.

A karshe, Shugaban KECI ya bukaci masu rajin kafa Jihar Gurara, musamman daga Kudancin Kaduna, da su daina kokarin saka Masarautar Kauru cikin sabon tsarin jihar, yana mai bukatar a girmama ra’ayin jama’ar yankin.

Cov/Jibirin Zaria

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dalilin Nijeriya Na Karbo Bashin Dala Biliyan 12 Daga Kasar Japan
  • Shugaban Hukumar Makamashin Nukliya Ta Kasar Iran Ya Ce Dukka Ayyukan Makamashin Nukliya A Cikin Gida Suna Tafiya Da Karfinsu
  • Masarautar Kauru Ta Bayyana Rashin Sha’awarta Kan Shiga Sabuwar Jihar Gurara
  • Waraka Daga Bashin Ketare
  • Netanytahu Ya Fusta Da Furucin Kasar Canada Akan Kisan Kiyashi A Gaza
  • Yadda masu safarar ɗan Adam ke yaudarar mutane ta intanet
  • Sin Ta Kara Wasu Kamfanonin Amurka 12 Cikin Jerin Wadanda Ta Dakatar Da Fitar Musu Da Wasu Kayayyaki Daga Kasar Sin
  • Sharhin Bayan Labarai: Yakin Kasuwanci Tsakanin Amurka da Kasashen Duniya
  • Sin Ta Kara Buga Haraji Kan Kayayyakin Da Ake Shigarwa Kasar Daga Amurka Zuwa 84%
  • Tattalin Arzikin Sin Na Bunkasa Yadda Ya Kamata Duk Da Kakkaba Mata Karin Harajin Kwastam Daga Amurka