Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-04-12@04:10:27 GMT

NAHCON Za Ta Fara Jigilar Alhazai Ranar 5 Ga Watan Mayun 2025

Published: 12th, March 2025 GMT

NAHCON Za Ta Fara Jigilar Alhazai Ranar 5 Ga Watan Mayun 2025

Hukumar Alhazai ta Kasa NAHCON ta fitar da sunayen kamfanonin jiragen sama da za su yi jigilar Alhazan bana.

Bayanin ya ƙunshi sunayen jiragen da kuma adadin mahajjatan da aka ware wa kowannensu.

Kamfanin Fly Nas zai yi jigilar Alhazai 22,893, kashi 32.12 bisa dari kenan na maniyyatan Najeriya a bana, yayin da Kamfanin Air peace ya sami Alhazai  9,145 , kashi 12.

83.

Sauran su ne Max Air Ltd da aka warewa Alhazai 23,343, kashin 32.75 kenan bisa dari, sai kamfanin Umza Air Ltd an ware  da ya sami 15,893 wato kashi 22.30 bisa 100, wanda ya kawo adadin maniyyata 71,274 da ake sa ran za su sauke farali a bana.

Hukumar ta NAHCON ta ce za a fara jigilar maniyyatan ne a ranar 5 ga Mayun 2025.

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigilar Maniyyata

এছাড়াও পড়ুন:

Kasashen China Da EU Sun Maida Martani Kudin Fito Kan Kasar Amurka

Kasashen China da Tarayyar Turai sun maida martani kan kudaden fiton da Amurka ta kara masu.

Kamfanin dillancin labaran Rauter ya bayyana cewa kasashen Turai 27 sun kara kashi 25% ga wasu zababbun kayakin kasar Amurka masu shigowa kasashen su. Wannan dais hi ne maida martani na farko wanda kasashen turan suka yi tun bayan da gwamnatin shugaba Trump ta kara kudaden fito ga kasashen duniya da dama wadanda suka hada da China da kuma kasashen turai EU.

Labarin ya kara da cewa karin kudaden fiton sun shafi motoci da karfe da kuma karfen alminium ne da suke shigo da su daga kasar ta Amurka ne.  Banda haka karin kudaden fiton sun shafi kayakin abinci wadanda suka hada da waken soya, kayan zaki, shinkafa lemun zaki,  almonds,  taba da kuma wasu ababen hawa da kuma Kannan kwalekwale.

Jimillar kayakin da abin ya shafa zai kai Uro billiyon 22.1. sai dai wannan bai kai Euro billiyon 26 wanda gwamnatin Amurka ta karawa kasashen na turai ba.

Labarin ya kammala da cewa sabon kudaden fito na kayakin Amurkan zai fara aiki a ranar talata 15 ga watan Afrilun da muke ciki, wasu kuma 16 ga watan Mayu da kuma wasu a ranar 1 ga watan Decemba karshen wannan shekara.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hisbah ta warware rigingimu 565 da lalata katan 51 na barasa a Yobe
  • Gwamnatin Sakkwato na biyan mafi ƙarancin albashin N70,000 – NLC
  • Kasashen China Da EU Sun Maida Martani Kudin Fito Kan Kasar Amurka
  • Trust Radio 92.7FM za ta fara shirye-shiryen gwaji
  • Jami’an Amurka da na Saudiyya sun tattauna batutuwan da suka shafi Gaza da yankin
  • E.U.  ta dauki wasu sabbin matakan kalubalantar harajin fito na Amurka
  • Macron :  Faransa na shirin amincewa da yankin Falasdinawa a matsayin kasa
  • Trump ya janye harajin da ya kara wa duniya, amma ya laftawa China 125%
  • Hajjin 2025: Jihar Kaduna Ta Yi Tanadin Masauki Na Musamman Ga Alhazan Bana
  • Amurka Ta Ƙara Wa Kayayyakin China Haraji Zuwa Kashi 104