Jami’an tsaro a kasar Pakistan sun kubutar da mutane 155 daga cikin fasinjoji kimani 450 wadanda yan bindigan daga kungiyar ‘Baloch Liberation Army (BLA) suke garkuawa da su tun jiya, wadanda suka yi barazanar kashesu, idan gwamnatin Islamabad bata biya masu bukatunsu ba.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto majiyar jami’an tsaro na kasar ta Pakisatan na cewa ya zuwa yanzu sun halaka yan bindiga 27.

Sannan suna shirin kubutar da sauran nan gaba. Labarin ya kara da cewa daga cikin wadanda aka kubutar akwai mata da yara.

Kafin haka dai a jiya Talata ce yan bindiga na kungiyar BLA suka tsare wani jirgin fasinja mai suna ‘Jaffar Express’ dauke da fasinjoji 450 daga garin Quetta zuwa Peshawar.

Manufar garkuwan dai ita ce neman gwamnatin Pakisatn ta bawa yankin Baluchistan na kasar Pakisatan yencin kanta a matsayin kasa mai zaman kanta.

Labarin ya ce yan bindigan sun ta da nakiya ne suka lalata layin dogon, kafin su tilastawa Jirgin tsayawa.

Ya zuwa yanzu dai yan bindigan sun kashe mutane 3 daga cikin har da direban jirgin.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

HOTUNA: Fashewar tankar gas ta kashe gomman mutane a Legas

Wata tanka ɗauke da gas ta yi bindiga a Jihar Legas da ke kudu maso yammacin Nijeriya, lamarin da ya yi sanadin mutuwar gomman mutane da jikkata da dama.

Lamarin ya faru ne a ranar Talata da dare a ƙarƙashin gadar mota ta Otedola, wadda tana daga cikin manyan hanyoyin da ke haɗe Legas da sauran sassan ƙasar.

HOTUNA: An hana Gwamna Fubara shiga Majalisar Dokokin Ribas Ukraine ta amince da ƙudurin tsagaita wuta a fafatawarta da Rasha

Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne a lokacin da tankar ke ƙoƙarin juyawa domin kai gas ɗin wani gidan mai, inda a nan ne ta faɗi ta yi bindiga.

Mutane da dama da suka shaida lamarin sun ce ya ƙazanta, sakamakon yadda wuta ta kama motoci da dama da kuma gidaje da ke kusa.

Wakilin kamfanin dillancin labarai na Anadolu ya tattauna da wani mutum da ya tsira da ransa sakamakon lamarin.

“Tankar ta faɗo kan motata, inda ta tura ta gefen hanya. Sai na yi sauri na gudu bayan na gano cewa gas ne, sai tankar ta yi bindiga cikin ƙasa da minti uku,” in ji Ajayi Segun, wanda ya rasa motarsa ƙirar Sienna sakamakon faruwar lamarin.

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Legas, Benjamin Hundeyin, a wani rahoto na wucin-gadi da ya fitar ya tabbatar da cewa lamarin ya rutsa da gidaje huɗu tare da haka kuma motoci 15 sun ƙone ƙurmus.

“Ana zargin hatsarin ya afku ne a lokacin da motar ke kokarin hawan hanyar Legas zuwa Ibadan ta gadar Otedola,” inji shi.

“Saboda haka, motar ta kife a kan hanya sannan ta yi bindiga nan take.”

“Har yanzu ana kididdige adadin rayukan mutanen da aka rasa, domin an gano gawawwaki biyu ne kawai.

“Lamarin ya kuma shafi wani asibiti mai zaman kansa, sai dai har yanzu babu cikakken bayani game da halin da waɗanda lamarin ya shafa a can.

“Za a ci gaba da bayar da rahoto a yayin da ake ci gaba da aikin ceto,” kamar yadda ya bayyana.

Jami’in Hukumar Agajin Gaggawa na Kasa (NEMA) shiyyar Kudu maso Yamma, Ibrahim Farinyole, ya tabbatar da faruwar lamarin da cewa suna ci gaba da ƙididdige asarar da aka yi.

A cewarsa, mutum daya ya mutu yayin da wasu hudu suka jikkata baya ga motoci 14 da shaguna hudu da suka ƙone ƙurmus.

A cikin ‘yan watannin nan, an samu fashewar tankokin mai dama a Nijeriya inda kusan mutum 300 suka rasu a ƙasar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Pakisatan: An Kubutar Da Mutane 155 Sannan Yan Ta’adda 27 Sun Halaka  A Garkuwan Jirgin Fasinja A Jiya Talata
  • Ministan Yaki Na HKI Yace Sojojin HKI Zasu Ci Gaba Da Zama A Kasar Siriya Har’abada
  • Dan ta’adda zai biya tarar miliyoyi bayan shan dukan kawo wuka a Katsina
  • HOTUNA: Fashewar tankar gas ta kashe gomman mutane a Legas
  • Sojoji Sun Miƙawa Gwamnatin Borno Mutane 75 Da Suka Ceto
  • Gina Mutane Don Bunkasa Hazakarsu Na Daga Cikin Ajendar Sin Na 2025
  • Abin da ya sa na sauya sheƙa daga APC zuwa SDP — El-Rufai
  • Sama da mutane 1,000 suka mutu a rikicin Siriya
  • Tawagar Majalisar Dinkin Duniya na rangadi a wuraren da aka aikata kisan kiyashi a Syria