Leadership News Hausa:
2025-04-12@07:25:50 GMT

Wata Miyar Sai A Makwabta…

Published: 13th, March 2025 GMT

Wata Miyar Sai A Makwabta…

Idan ka dauki bangaren tsofaffi da kananan yara, za ka iya cewa su ne mafi rauni a cikin al’umma. Tsofaffi sun gajiya don haka suna bukatar taimako, yara kanana kuma ba su kawo karfi ba, bisa haka dole suna bukatar madafa. A nan, sai mu ce gwamnatin Sin ta yi tunani mai kyau.

Kundin rahoton ya kuma bayyana cewa, a shekarar 2025 gwamnatin kasar za ta kara zage damtse wajen raya kauyukan dake rabe da birane da gyara gine-ginen da suka tsufa.

Ga duk wanda yake shiga yankunan kauyuka da ke cikin birane (kamar unguwannin masu karamin karfi) ko wadanda suke rabe da su zai ga ba su da kyawun gani, domin kayayyakin alatu da kayatattun gine-gine da ababen more rayuwa da ake samarwa a cikin birane ba za su taba bari taurarin wadannan kauyuka su haska ba. Domin tabbatar da ci gaba da zamanintar da kasar Sin yadda ya kamata, dole ne a tafi tare da ire-iren wadannan kauyuka cikin ayyukan ci gaba da ake gudanarwa.

Har ila yau, rahoton ayyukan gwamnatin ya bayyana cewa, a bana, gwamnatin kasar ta kudiri aniyar kara yawan kudin tallafin muhimman ayyukan inshorar kiwon lafiya ga mazauna karkara da marasa aikin yi na birane, inda aka kara yawan kudin da yuan 30 ga kowane mutum. Ko tantama babu, tabbas wannan zai kara inganta kiwon lafiyar al’umma musamman marasa karfi.

Bugu da kari, tallafin kiwon lafiyar bai tsaya nan ba, akwai wani kaso na musamman da gwamnatin za ta ware na tallafin kudin kiwon lafiya ga daukacin al’umma a bangaren muhimman bukatunsu inda shi ma aka kara yawansa da yuan 5 ga kowane mahaluki da zai ci gajiya.

Baya ga batun tallafi na zuwa asibiti, gwamnatin ta kuma yi wata farar dabara da za ta kara inganta koshin lafiya ta hanyar sanya gina dandaloli da dakunan wasannin motsa jiki a kusa da gidajen al’umma a cikin kundin rahoton ayyukanta na 2025. Wannan dabara za ta kara inganta kiwon lafiyar al’umma saboda kowa ya san yadda motsa jiki ya zama wajibi ga duk wanda yake son samun koshin lafiya.

Kazalika, da yake zamani na ci gaba da sauyawa ta fuskar komai da komai, gwamnatin kasar Sin ta sha alwashin hanzarta komawa amfani da tsarin biyan kudade na zamani da aka inganta domin kara saukaka hada-hada da harkokin kudade.

Duka wadannan abubuwa an bullo da su ne domin cimma muradun jama’a da kara kula da bukatunsu. A gaskiya ina kwadayin ganin irin wannan tsari a kasashenmu na Afirka, saboda muhimmanta bukatun jama’a alhaki ne da ke rataye a wuyar gwamnati. Ya kamata shugabanninmu su sa himma da kwazo don su raba mu da tunanin “wata miyar sai a makwabta”, a duk lokacin da muka ga yadda ake kula da muradun al’umma a wasu kasashe, musamman kasar Sin. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: kiwon lafiya

এছাড়াও পড়ুন:

Hisbah Ta Lalata Katan 51 Na Giya a Jihar Yobe

Ya ce shan giya yana barazana ga lafiyar jama’a tare da haddasa matsalolin zamantakewa.

A cewarsa, hana yaɗuwar giya zai rage aikata laifuka da kuma inganta zaman lafiya.

Dr. Yahuza ya kuma buƙaci al’umma da su mara wa Hisbah baya ta hanyar bayar da rahoto kan duk wani abu da ke saɓa wa doka.

Ya tabbatar da cewa hukumar ta ƙudiri aniyar ci gaba da aiki don tabbatar da adalci, zaman lafiya da gyara halayyar al’umma a Jihar Yobe.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hisbah Ta Lalata Katan 51 Na Giya a Jihar Yobe
  • Uwargidan Shugaban Kasa Ta Ba Matan Arewa Ta Gabas Su Dubu Tallafin Naira Miliyan 50
  • Za a mayar da tubabbun ’Yan Boko Haram cikin al’umma – Gwamna Buni
  • UBEC Ta Yaba Wa Jigawa Kan Inganta Harkar Ilimi A Jihar
  • Sin Ta Bayyana Wani Shiri Na Bunkasa Kiwon Lafiya
  • Femi Falana SAN Ya Yi Kiran A Inganta Harkar Shari’a A Najeriya
  • Gwamnatin Kano Ta Fidda Sabbin Dokoki Domin Yaƙi Da Gurɓata Muhalli
  • Sin Ta Kara Buga Haraji Kan Kayayyakin Da Ake Shigarwa Kasar Daga Amurka Zuwa 84%
  • China Ta Karawa Kayakin Masu Shiga Kasar Kudaden Fito Har Zuwa Kashi 84%
  • Xi Ya Yi Kira Da A Gina Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Tare Da Kasashe Makwabta