Rasha na goyon bayan sake farfado da yarjejeniyar nukiliyar Iran
Published: 13th, March 2025 GMT
Ministan harklokin wajen Rasha, Sergei Lavrov ya ce kasarsa na goyon bayan sake farfado da yarjejeniyar farko ta Iran da kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya ya amince da shi.
Mista Lavrov ya jaddada goyon bayan Moscow ga sake farfado da muhimmiyar yarjejeniya da Iran da manyan kasashen duniya suka rattabawa hannu a shekarar 2015.
“Mun tattauna halin da ake ciki a yankin Tekun Fasha da kuma shirin hadin gwiwa,” in ji Lavrov a wata hira, a cewar kamfanin dillancin labarai na Tass, yayin da yake amsa tambaya kan ko batun Iran na cikin tattaunawar da ake yi tsakanin Rasha da Amurka.
Rasha ta tattauna halin da ake ciki dangane da yarjejeniyar da Iran ta kulla da Amurka yayin da ta ci gaba da tattaunawa kan batun da kasashen Turai, yana mai jaddada maido da yarjejeniyar da ake yi a halin yanzu “wanda Amurkawa suka balle a lokacin gwamnatin Trump ta farko.” »
Lavrov ya bayyana cewa “Rasha za ta goyi bayan ci gaba da tsarin da ya samar da ainihin yarjejeniyar da kwamitin sulhu da Iran suka amince da ita. »
“Za mu ga yadda lamarin zai kasance,” in ji shi, yayin da yake magana kan shawarwarin da ya yi da jami’an Amurka da na Turai.
Ministan harkokin wajen na Rasha ya kuma yi magana kan rahotannin kafafen yada labaran kasashen yammacin duniya da ke nuni da cewa shugaban Amurka Donald Trump ya yi kira da a kulla sabuwar yarjejeniyar nukiliya a wata wasika da ya aike zuwa Tehran.
“Amurka na son sabuwar yarjejeniyar nukiliya da Iran don tilasta mata kada ta goyi bayan kungiyoyin da ke gabas ta tsakiya, amma wannan zabin ba zai yi tasiri ba. “Abin damuwa ne yadda Amurkawa su sanya sharuddan siyasa ga wannan sabuwar yarjejeniya,” in ji shi.
Lavrov ya kuma yi watsi da duk wani matsin lamba ga Iran kan tasirin da take da shi a yammacin Asiya.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: da yarjejeniyar
এছাড়াও পড়ুন:
Iran: Akwai damammaki na diflomasiyya da za mu jarraba aniyar Amurka a kansu
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Esmaeil Baqaei ya bayyana cewa, ma’a, kwana guda gabanin tattaunawar da ake jira a kasar Oman tsakanin Amurka da Iran kan shirin nukiliyar kasar Iran, damammaki da daman a diflomasiyya da Amurka za ta iya tabbatar da aniyarta a kansu
Baqaei ya rubuta a dandalin X, “Ya kamata Amurka ta mutunta wannan shawarar da aka yanke duk da cewa ana fama da rikici.”
“Ba za mu yanke hukunci ba, Muna da niyyar tantance niyyar dayan bangaren kuma za mu tabbatar da hakan a wannan Asabar,” in ji jami’in diflomasiyyar na Iran, ya kara da cewa Iran “za ta yi tunani kuma ta mayar da martani ga kowane mtaki.”
A ranar Litinin shugaban Amurka Donald Trump ya ba da sanarwar cewa gwamnatinsa za ta shiga tattaunawa da Iran.
A ci gaba da tattaunawar da za a yi a ranar Asabar, bangarorin biyu sun yi musayar kalamai masu zafi, inda Trump ya yi barazanar daukar matakin soji idan tattaunawar ta ci tura.
Dangane da gargadin na Trump, wani babban mataimaki ga jagoran Iran Ayatollah Sayyed Ali Khamenei ya ce Iran za ta iya daukar matakan da duk ta ga sun dace a kan wannan lamari.
Taron na ranar Asabar na zuwa biyo bayan wata wasika da Trump ya aikewa Sayyed Khamenei a watan da ya gabata, inda ya bukaci Tehran da ta shiga tattaunawa tare da yin gargadin cewa matakin soji na kan teburi idan Iran ta ki amincewa.
Tehran ta bayyana aniyar ta na shiga tattaunawar kai tsaye amma muddin Washington ta ci gaba da manufofinta na “mafi girman matsin lamba”.