Rasha na goyon bayan sake farfado da yarjejeniyar nukiliyar Iran
Published: 13th, March 2025 GMT
Ministan harklokin wajen Rasha, Sergei Lavrov ya ce kasarsa na goyon bayan sake farfado da yarjejeniyar farko ta Iran da kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya ya amince da shi.
Mista Lavrov ya jaddada goyon bayan Moscow ga sake farfado da muhimmiyar yarjejeniya da Iran da manyan kasashen duniya suka rattabawa hannu a shekarar 2015.
“Mun tattauna halin da ake ciki a yankin Tekun Fasha da kuma shirin hadin gwiwa,” in ji Lavrov a wata hira, a cewar kamfanin dillancin labarai na Tass, yayin da yake amsa tambaya kan ko batun Iran na cikin tattaunawar da ake yi tsakanin Rasha da Amurka.
Rasha ta tattauna halin da ake ciki dangane da yarjejeniyar da Iran ta kulla da Amurka yayin da ta ci gaba da tattaunawa kan batun da kasashen Turai, yana mai jaddada maido da yarjejeniyar da ake yi a halin yanzu “wanda Amurkawa suka balle a lokacin gwamnatin Trump ta farko.” »
Lavrov ya bayyana cewa “Rasha za ta goyi bayan ci gaba da tsarin da ya samar da ainihin yarjejeniyar da kwamitin sulhu da Iran suka amince da ita. »
“Za mu ga yadda lamarin zai kasance,” in ji shi, yayin da yake magana kan shawarwarin da ya yi da jami’an Amurka da na Turai.
Ministan harkokin wajen na Rasha ya kuma yi magana kan rahotannin kafafen yada labaran kasashen yammacin duniya da ke nuni da cewa shugaban Amurka Donald Trump ya yi kira da a kulla sabuwar yarjejeniyar nukiliya a wata wasika da ya aike zuwa Tehran.
“Amurka na son sabuwar yarjejeniyar nukiliya da Iran don tilasta mata kada ta goyi bayan kungiyoyin da ke gabas ta tsakiya, amma wannan zabin ba zai yi tasiri ba. “Abin damuwa ne yadda Amurkawa su sanya sharuddan siyasa ga wannan sabuwar yarjejeniya,” in ji shi.
Lavrov ya kuma yi watsi da duk wani matsin lamba ga Iran kan tasirin da take da shi a yammacin Asiya.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: da yarjejeniyar
এছাড়াও পড়ুন:
Jagora : kiran Trump, na tattaunawa Da Iran yaudarar duniya ne
Jagoran juyin juya halin Musulunci na Iran, Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya ce kiran da shugaban Amurka Donald Trump ya yi na tattauanwa da Iran ba komai ba ne illa wani yunkuri na yaudarar al’ummar duniya.
“Mun zauna tsawon shekaru muna tattaunawa, mun zamna da su teburin tattaunawa, bayan hakan shi wannan mutumin ya yayyaga yarjejeniyar da aka sanya wa hannu,” kamar yadda jagoran ya bayyana yayin da yake jawabi ga taron dalibai a birnin Tehran a jiya Laraba.
“tunda mu ka ga baya girmama yarjejeniya, menene ma’anar yin shawarwari kuma ?”
“Saboda haka, kiraye-kirayen yin shawarwarin da tattaunawa na da nufin yaudarar jama’a na duniya.” Inji jagoran.
Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya ce “Idan manufar tattaunawar ita ce a dage takunkumin, yin shawarwari da wannan gwamnatin Amurka, ba za ta cire takunkumin ba. Hakan zai sa takunkumin ya kara tsananta tare da kara matsin lamba,” in ji Jagoran.
Yayin da yake mayar da martani kan zargin da kasashen yammacin duniya ke yi na cewa Tehran na neman makaman nukiliya, Jagoran ya sake jaddada cewa Iran ba ta son kera makaman kare dangi, inda ya kara da cewa da ta yi niyyar yin hakan da ta yi shi ya zuwa yanzu.
“An ce ‘ba za mu bar Iran ta samu makaman nukiliya ba.’ Da muna son kera makaman nukiliya, da Amurka ba za ta hana mu ba.
Gaskiyar ita ce ba mu da makaman nukiliya, saboda mu da kanmu ba ma son su saboda wasu dalilai.”