HausaTv:
2025-04-13@09:52:26 GMT

Jagora : kiran Trump, na tattaunawa Da Iran yaudarar duniya ne

Published: 13th, March 2025 GMT

Jagoran juyin juya halin Musulunci na Iran, Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya ce kiran da shugaban Amurka Donald Trump ya yi na tattauanwa da Iran ba komai ba ne illa wani yunkuri na yaudarar al’ummar duniya.

 “Mun zauna tsawon shekaru muna tattaunawa, mun zamna da su teburin tattaunawa, bayan hakan shi wannan mutumin ya yayyaga yarjejeniyar da aka sanya wa hannu,” kamar yadda jagoran ya bayyana yayin da yake jawabi ga taron dalibai a birnin Tehran a jiya Laraba.

“tunda mu ka ga baya girmama yarjejeniya, menene ma’anar yin shawarwari kuma ?”

“Saboda haka, kiraye-kirayen yin shawarwarin da tattaunawa na da nufin yaudarar  jama’a na duniya.” Inji jagoran.

Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya ce “Idan manufar tattaunawar ita ce a dage takunkumin, yin shawarwari da wannan gwamnatin Amurka, ba za ta cire takunkumin ba. Hakan zai sa takunkumin ya kara tsananta tare da kara matsin lamba,” in ji Jagoran.

Yayin da yake mayar da martani kan zargin da kasashen yammacin duniya ke yi na cewa Tehran na neman makaman nukiliya, Jagoran ya sake jaddada cewa Iran ba ta son kera makaman kare dangi, inda ya kara da cewa da ta yi niyyar yin hakan da ta yi shi ya zuwa yanzu.

“An ce ‘ba za mu bar Iran ta samu makaman nukiliya ba.’ Da muna son kera makaman nukiliya, da Amurka ba za ta hana mu ba.

Gaskiyar ita ce ba mu da makaman nukiliya, saboda mu da kanmu ba ma son su saboda wasu dalilai.”

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: makaman nukiliya

এছাড়াও পড়ুন:

Fadar Mulkin Amurka: Tattaunawa Da Iran Ta Yi Armashi

Fadar mulkin Amurka ta “White Hosue” ta bayyana cewa tattaunawar da aka yi a tsakanin ministan harkokin wajen Iran Abbas Arakci  da wakilin Donald Trump akan gabas ta tsakiya Steve Witkoff, ta hanyar shiga tsakanin kasar Oman, ta yi armashi.

Da marecen jiya Steve Witkoff ya bayyana cewa; shugaba Donald Trump ya ba shi umarnin ya yi duk abinda zai iya domin rage tazarar sabanin da ake da ita ta hanyar tattaunawa da diflomasiyya.

Bayanin na fadar mulkin Amurka ya kuma yaba wa kasar Oman wacce ta kasance mai masaukin baki na tattaunawar da aka yi wacce ba ta gaba da gaba ba ce a tsakanin Amurkan da kuma Iran.

Gabanin bayanin na fadar mulkin Amurkan, manzon musamman na shugaba Donald Trump, Steve Witkoff ya fada wa tashar talabijin din NBC cewa, ya yi tattaunawa mai matukar armashi da kuma amfani.

Tun a ranar Asabar da safe ne dai ministan harkokin wajen na Iran Abbas Arakci ya isa birnin Mascut, inda ya gana da takwaransa na kasar Sayyid Hamad Bin Hamud al-Busa’idi, tare da mika masa bayanai da su ka kunshi mahangar Iran akan tattaunawar.

Ministan na harkokin wajen Oman ya zama mai shiga tsakanin kasashen biyu a tsawon lokacin tattaunawar. Bangarorin biyu sun yi musayar takardu har sau hudu.

A ranar Asabar mai zuwa ne dai za a ci gaba da tattaunawar daga inda aka tsaya a wani wurin da ba a kai ga ayyana shi ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Fadar Mulkin Amurka: Tattaunawa Da Iran Ta Yi Armashi
  • Sharhi: Tattaunawa Zagaye Na Farko Tsakanin Iran Da Amurka A Oman
  • Kasashen duniya da kungiyoyin kasa da kasa na fatan nasara ga tattaunawar Amurka da Iran
  • Iran da Amurka zasu ci gaba da tattaunawa a mako mai zuwa
  •  Limamin Tehran: Iran Ba Ta Tsoron Tattaunawa
  • Iran: Akwai damammaki na diflomasiyya da za mu jarraba aniyar Amurka a kansu
  • Pezeshkian : Jagora bai shi da adawa da Amurkawa masu zuba jari a Iran
  • Amurka ta laftawa Iran sabbin takunkumai gabanin tattaunawar Oman
  • Trump ya janye harajin da ya kara wa duniya, amma ya laftawa China 125%
  • Trump Ya Dakatar da Harajin Da Sanya Wa Ƙasashen Duniya, Ya Ƙi Cire Wa China