Gwamna Nasir Idris na jihar Kebbi, ya ba da umarnin cewa, wadanda harin da ‘yan bindiga suka kai a sansanin ‘yan gudun hijira da ke karamar hukumar Arewa ta jihar, su koma gidajensu nan da makonni biyu masu zuwa bayan an dauki matakai a yankunan da lamarin ya shafa.

 

Gwamnan, ya ba da umarnin ne a lokacin da ya kai ziyarar jaje sansanin ‘yan gudun hijira da ke Kangiwa da Lakurawa suka kai musu hari tare da raba su da muhallansu a kauyukan Birnin Debe, Dan Marke da Tambo.

 

Gwamnan ya ce, ya kai ziyarar ne domin jajanta wa wadanda abin ya shafa tare da ba shi damar samun rahoton halin da ake ciki a kan wannan mummunan lamari don jagorantar gwamnatin jihar ta dauki matakin da ake bukata tare da tantance halin da ake ciki da kuma tabbatar da matakan da suka dace da za a dauka cikin gaggawa domin kai daukin gaggawa ga wadanda abin ya shafa.

 

A yayin da yake koka da cewa, ana kai hare-haren ne daga jihar Sokoto da ke makwabtaka da Jamhuriyar Nijar, Gwamnan ya nuna rashin jin dadinsa kan asarar rayuka da dukiyoyi da aka yi, ya kuma yaba wa jami’an tsaro da suka yi iya kokarinsu wajen ganin an shawo kan lamarin, ya kuma bukaci jama’a da su rika kai rahoton duk wani motsi da suka samu ga hukuma domin daukar matakin da ya dace.

 

Tun da farko Shugaban Karamar Hukumar Arewa Alhaji Sani Aliyu ya godewa Gwamnan bisa daukar matakin gaggawa don ganin an shawo kan wannan mummunan lamari.

 

Shugaban ya kuma bayyana cewa an bayar da agajin ga wadanda abin ya shafa, inda ya ce iyalan kowannen wadanda suka rasa rayukansu sun samu Naira 500,000 yayin da kowanne daga cikin wadanda suka jikkata kuma ya samu N500,000.

 

A ranar Lahadin da ta gabata ne ‘yan bindigar Lakurawa suka kai hari kauyuka 7 a karamar hukumar Arewa ta jihar Kebbi inda suka kashe sama da mutane 10 tare da kona gidaje da dama wanda hakan ya kasance harin ramuwar gayya biyo bayan kashe wani shugabansu mai suna Maigemu da jami’an tsaro suka yi.

 

 

Abdullahi Tukur

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Gwamna Lakurawa

এছাড়াও পড়ুন:

Ko dai Gwamna Fubara ya yi murabus ko a tsige shi — APC

Jam’iyyar APC ta yi kira ga Gwamnan Ribas, Siminalayi Fubara da ya sauka daga mulki ko kuma a tsige shi.

Shugaban APC na Jihar Ribas, Tony Okocha ne ya bayyana haka yayin zantawa da manema labarai yau Litinin a birnin Fatakwal.

An cafke mutum uku kan satar wayoyin lantarki a Adamawa Abin da ya sa na sauya sheƙa daga APC zuwa SDP — El-Rufai

Okocha ya ce gayyatar da Fubara ya aika wa ’yan majalisar dokokin jihar domin ya gana da su akwai lauje cikin naɗi.

“Hukuncin Kotun Ƙoli ne ƙarshe babu wani abu da wani zai iya yi. Abun da ya rage wa gwamnan shi ne ko dai ya sauka, ko kuma a tsige shi,” in ji Okocha.

Tun da farko, bayan hukuncin kotun ƙolin, majalisar jihar ta ba gwamnan jihar wa’adin kwana biyu ya sake gabatar da kasafin kuɗi, gayyatar da ya ƙi amsawa.

Daga baya shi kuma gwamnan ya gayyace su gidan gwamnati domin su tattauna, inda su ma suka ce ba za su je ba, domin a kafofin sadarwa suka ga gayyatar.

Ana iya tuna cewa, majalisar ta kuma bai wa Gwamna Fubara wa’adin sallamar da sau naɗe-naɗen da ya yi wanda ba ita ta tantance su ba.

Za a sake zaɓen ƙananan hukumomin Ribas

A makon jiya ne Hukumar zaɓen Rivers ta saka 9 ga watan Agusta a matsayin ranar sake zaɓen ƙananan hukumomi.

Rahotonni sun ambato shugaban hukumar Adolphus Enebeli na sanar da hakan yayin wata ganawa da masu ruwa da tsaki a birnin Fatakwal.

Wannan na zuwa ne bayan Kotun Ƙolin Nijeriya ta soke zaɓen da hukumar ta gudanar a ranar 5 ga watan Oktoban 2024.

A gefe guda kuma, majalisar dokokin jihar ta gayyaci shugaban hukumar ya bayyana a gabanta domin yin bayani game da zaɓen.

Wannan dambarwar na zuwa ne a yayin da rikicin siyasa tsakanin gwamnan da tsohon gwamna kuma Ministan Abuja, Nyesom Wike, ke ƙara kamari.

Tun bayan ɗarewar Fubara kan mulki, dangantakar da ke tsakaninsa da magabacinsa ta yi tsami, lamarin da ya haddasa rabuwar kawuna a Majalisar Dokokin jihar.

Wasu ‘yan majalisa sun tsaya tsayin daka domin kare gwamnan, yayin da wasu ke goyon bayan APC da Wike.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gidauniyar Bafarawa Ta Rabawa Kananan ‘Yan Kasuwa Naira Milliyan 13 a Sokoto
  • Ruwan Sama Ya Lalata Gidaje Da Makarantu A Jihar Kwara
  • Pakisatan: An Kubutar Da Mutane 155 Sannan Yan Ta’adda 27 Suka Halaka  A Garkuwan Jirgin Fasinja A Jiya Talata
  • Pakisatan: An Kubutar Da Mutane 155 Sannan Yan Ta’adda 27 Sun Halaka  A Garkuwan Jirgin Fasinja A Jiya Talata
  • Majalisar Wakilai ta ba da umarnin rufe shafukan intanet na batsa
  • Lakurawa sun kashe mutum 13 a ƙauyukan Kebbi
  • Hamas : tattaunawa ce kawai mafita ta sakin wadanda ake garkuwa dasu
  • Harin Lakurawa: An Kashe Mutane 15 Tare Da Kona Kauyuka 7 A Birnin Kebbi
  • Ko dai Gwamna Fubara ya yi murabus ko a tsige shi — APC