Hukumar kula da tituna ta tarayya (FERMA) ta jaddada kudirinta na kula da titunan gwamnatin tarayya da inganta ababen more rayuwa a fadin kasar nan.

 

Daraktan hukumar ta FERMA, Injiniya Kabiru Iliyasu Dan-Mulki ne ya bayyana haka a lokacin da ya karbi bakuncin shugabannin kungiyar ‘yan jarida ta kasa (NUJ) daga gidan rediyon tarayya (FRCN) da kuma gidan talabijin na Najeriya (NTA) Kaduna a ofishinsa da ke Kaduna.

 

Injiniya Dan-Mulki ya jaddada babban nauyin da ya rataya a wuyan hukumar ta FERMA na tabbatar da cewa titunan gwamnatin tarayya sun kasance masu kyau domin saukaka zirga-zirga a fadin kasar nan. Ya bayyana muhimmancin hada hannu da masu ruwa da tsaki, musamman kafafen yada labarai, domin wayar da kan jama’a game da ayyukan hukumar da kuma muhimmiyar rawar da take takawa wajen ci gaban kasa.

 

A nasu jawabin, shugaban kungiyar ta NUJ FRCN na Kaduna, Kwamared Umar Sarkin Fada, da sakataren kungiyar ta NUJ NTA Kaduna, Haruna Mohammed, sun jaddada bukatar hada kai wajen inganta ayyukan FERMA. Sun bayyana cewa ziyarar na da nufin karfafa hadin gwiwa wajen tallata ayyukan hukumar da karfafa gwiwar ‘yan kasar da su bayar da tasu gudummawar wajen kiyaye ababen more rayuwa.

 

Shugabannin kungiyar ta NUJ sun kuma bayyana damuwarsu kan rashin kyawun wasu hanyoyin gwamnatin tarayya da kuma harabar manyan cibiyoyin gwamnatin tarayya da suka hada da FRCN da NTA Kaduna. Sun bukaci FERMA da ta magance wadannan matsalolin a matsayin wani bangare na alhakinta na zamantakewa (CSR).

 

Sun yabawa hukumar ta FERMA bisa jajircewarta na kula da tituna tare da bada tabbacin hukumar na cigaba da bayar da goyon bayan kafafen yada labarai wajen sanar da ‘yan Najeriya kokarin da take yi na inganta ababen more rayuwa a fadin kasar.

 

Shamsuddeen Mannir Atiku

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: gwamnatin tarayya

এছাড়াও পড়ুন:

HKI Ta Jefa Boma-Bomai A Kan Asbiti Tilo Da Ya Rage Yake Aiki A Arewacin Gaza

Jiragen yakin HKI HKI sun yi ruwan boma-bomai kan astin Al-Ahli, asbiti tilo da ya rage yake aiki a arewacin zirin Gaza, a safiyar yau Lahadi.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta bayyana cewa jiragen yakin HKI sun wargaza bangaren ’emagencu’ bukatar kula na gaggawa a asbitin da kuma kofar shiga asbitin. Har’ila yau hare-haren sun lalata bangaren Iskar Oxigen na kula da wadanda suke bukatar kula mai tsanani a asbiti. Kuma sanadiyyar haka mutane da dama sun rasa rayukansu awannan bangaren daga ciki har da wani yaro dan shekara 12 wanda ya ji rauni a kai.

Razan Al-Nahhas wani likita mai aiki a bangaren  kula na gaggawa a asbitin ya fadawa kafafen yada labarai kan cewa wannan asbitin ne kawai dama yake aiki a arewacin Gaza, kuma a halin yanzu babu wani asbitin da ya rage a yankin.

Labarin ya kara da cewa bayan  wadannan hare-hare kan asbitin na Al-Ahli, mutane da dama basu san inda zasu je don samun jinya ba.

Likitan ta kara da cewa kafin hare-hare na safiyar yau Lahadi dai marasa lafiya wadanda aka yankewa kafafu da kuma wadanda suka ji rauni a kai da kuma kirjinsu ne suka fi yawa a cikinsa. Sannan a halin yanzu babu inda zasu je sai wasu kananan asbitoci wadanda basu da kayakin aiki na kula da su. Kuma tuni wasu sun mutu bayan harin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • HKI Ta Jefa Boma-Bomai A Kan Asbiti Tilo Da Ya Rage Yake Aiki A Arewacin Gaza
  • Sin Ta Yi Allah-wadai Da Karin Harajin Amurka Ta Kuma Jaddada Goyon Bayanta Ga Ka’idojin WTO 
  • MDD: Mafi Yawancin Wadanda Yaki Ya Ci A Gaza Mata Ne Da Kananan Yara
  • Shugaban Hukumar Makamashin Nukliya Ta Kasar Iran Ya Ce Dukka Ayyukan Makamashin Nukliya A Cikin Gida Suna Tafiya Da Karfinsu
  • UBEC Ta Bayyana Jihar Jigawa A Matsayin Abin Kuyi A Fannin Ilimi
  • Masarautar Kauru Ta Bayyana Rashin Sha’awarta Kan Shiga Sabuwar Jihar Gurara
  • Tawagogin gwamnatin Kongo da kungiyar M23 sun isa  Doha domin tattaunawa
  • ’Yan kasuwa da dama sun mutu bayan kifewar kwalekwale a Kogin Neja
  • Gwamnati ta gargaɗi jihohi 30 kan ambaliyar ruwa
  • Yadda masu safarar ɗan Adam ke yaudarar mutane ta intanet