FERMA Ta Sake Jaddada Sadaukarwar Da Take Yi Na Kula Da Hanyoyin Tarayya
Published: 13th, March 2025 GMT
Hukumar kula da tituna ta tarayya (FERMA) ta jaddada kudirinta na kula da titunan gwamnatin tarayya da inganta ababen more rayuwa a fadin kasar nan.
Daraktan hukumar ta FERMA, Injiniya Kabiru Iliyasu Dan-Mulki ne ya bayyana haka a lokacin da ya karbi bakuncin shugabannin kungiyar ‘yan jarida ta kasa (NUJ) daga gidan rediyon tarayya (FRCN) da kuma gidan talabijin na Najeriya (NTA) Kaduna a ofishinsa da ke Kaduna.
Injiniya Dan-Mulki ya jaddada babban nauyin da ya rataya a wuyan hukumar ta FERMA na tabbatar da cewa titunan gwamnatin tarayya sun kasance masu kyau domin saukaka zirga-zirga a fadin kasar nan. Ya bayyana muhimmancin hada hannu da masu ruwa da tsaki, musamman kafafen yada labarai, domin wayar da kan jama’a game da ayyukan hukumar da kuma muhimmiyar rawar da take takawa wajen ci gaban kasa.
A nasu jawabin, shugaban kungiyar ta NUJ FRCN na Kaduna, Kwamared Umar Sarkin Fada, da sakataren kungiyar ta NUJ NTA Kaduna, Haruna Mohammed, sun jaddada bukatar hada kai wajen inganta ayyukan FERMA. Sun bayyana cewa ziyarar na da nufin karfafa hadin gwiwa wajen tallata ayyukan hukumar da karfafa gwiwar ‘yan kasar da su bayar da tasu gudummawar wajen kiyaye ababen more rayuwa.
Shugabannin kungiyar ta NUJ sun kuma bayyana damuwarsu kan rashin kyawun wasu hanyoyin gwamnatin tarayya da kuma harabar manyan cibiyoyin gwamnatin tarayya da suka hada da FRCN da NTA Kaduna. Sun bukaci FERMA da ta magance wadannan matsalolin a matsayin wani bangare na alhakinta na zamantakewa (CSR).
Sun yabawa hukumar ta FERMA bisa jajircewarta na kula da tituna tare da bada tabbacin hukumar na cigaba da bayar da goyon bayan kafafen yada labarai wajen sanar da ‘yan Najeriya kokarin da take yi na inganta ababen more rayuwa a fadin kasar.
Shamsuddeen Mannir Atiku
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: gwamnatin tarayya
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan sanda sun hallaka hatsabibin ɗan bindiga a Abuja
Rundunar ’Yan Sandan Babban Birnin Tarayya, ta kashe wani ƙasurgumin ɗan bindiga, Salisu Mohammed, wanda aka fi sani da Dogo Saleh, a wani artabu da suka yi da shi a dajin Gidan-Abe da ke kan iyakar Bwari da Kaduna.
Sun samu nasarar ne bayan samun bayanan sirri kan shigowar ‘yan bindiga yankin daga Kaduna.
NAJERIYA A YAU: Ko Sulhu Da ’Yan Ta’adda Zai Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Arewa? Hanyoyi 6 da mutum zai kare kansa daga tsananin zafiKwamishinan ’Yan Sandan Abuja, Olatunji Rilwan Disu, ya tabbatar da aukuwar lamarin, inda ya ce jami’an rundunar yaƙi da garkuwa da mutane, ƙarƙashin jagorancin Mustapha Muhammed, sun tare hanyar ’yan bindigar, inda suka yi musayar wuta da su.
“Mun yi nasarar kawar da barazana babba da ke addabar al’umma da hanyoyi,” in ji Disu.
An gano cewa Mohammed, mai shekaru 21, yana ɗaya daga cikin manyan ’yan bindigar da ke aiki a dajin Rijana na Kaduna.
“Ya sace mutane da yawa, ciki har da kashe jami’an tsaro da fararen hula.
“Jami’an tsaro sun ƙwato bindiga ƙirar AK-49, harsasai 60, da kuma Naira miliyan uku, da ake zargin kuɗin fansa ne da suka samu daga garkuwa da mutane,” in ji shi.
Bincike ya tabbatar da cewa ɗan bindigar na da hannu a kai hare-hare kauyukan Kike da Bagada, inda ya jagoranci garkuwa da mutane tare da karɓar kuɗin fansa.
“Ayyukansa sun jefa jama’a cikin fargaba, amma jami’anmu sun aika da saƙo mai ƙarfi cewa ba za a lamunci aikata laifi ba,” in ji Disu.
Wani jami’in ’yan sanda ya samu rauni kaɗan a yayin artabun, amma an ba shi kulawar da ya dace, inda yake murmurewa.
A halin yanzu, jami’an tsaro na ci gaba da farautar sauran ‘yan bindigar da suka tsere tare da rushe duk wani sansanin ’yan bindiga da ke iyakar Abuja da Kaduna.