Hukumar gudanarwar asibitin koyarwa na Aminu Kano ta ce ana kokarin ganin an dawo da ayyukan da masana’antar iskar Oxygen da asibitin ke yi.

 

A cewar Mataimakin Daraktan sashen (Biomedical/ kuma Shugaban Kwamitin Kula da Oxygen), Engr Ahmed Usman a madadin Hukumar, an sanya hannu kan wata yarjejeniya ta fahimtar juna tsakanin asibitin da Dodams Medical Equipt don kula da aikin na tsawon shekaru 2.

 

Ya bayyana cewa, a watan Janairun wannan shekara ne aka yi duk wani shiri da kuma biyan kudin jirgi, amma saboda hutun karshen shekara da Kamfanoni suka yi, an samu tsaiko wajen samar da wasu sassa musamman na’urar gudanarda aikin, wanda ya iso a ranar Litinin 10 ga Maris, 2025.

 

Ya ci gaba da cewa, tuni aka fara yi wa na’urar samar da iskar Oxygen aiki kamar yadda ya faru a jiya, wanda ya rage kawai na’urar kwampreso da kuma Oxygen buster, wadanda ke kan aiki.

 

A halin da ake ciki, a cikin wannan lokacin jirar Hukumar Kula da Asibitin ta fitar da iskar Oxygen a wani wuri musamman daga Kamfanin Loquat, kamar yadda ake yi a wasu asibitoci.

 

ABDULLAHI JALALUDDEEN KANO

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Babu Matsalar Da Za A Fuskanta Idan Majalisa Ta Tsige Fubara – Wike

Gwamna Fubara da Wike sun samu saɓani tun bayan hawa mulki, lamarin da ya haddasa rikici a siyasar Jihar Ribas, wacce ke da arziƙin man fetur.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Babu Matsalar Da Za A Fuskanta Idan Majalisa Ta Tsige Fubara – Wike
  • Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Ta Sha Alwashin Hukunta Masu Almundahana A Shirin Ciyarwar Azumi
  • Matashin da ke kera jiragen sama da bindigogi daga robobi
  • Sabon Kwamishinan ‘Yansanda Ya Kama Aiki A Kano
  • Sin Ta Gaggauta Aikin Gyara Da Kyautata Ababen Aikin Gona
  • Manyan makarantu sun shiga yajin aiki a Adamawa
  • EFCC Ta Kama ‘Yan China 4, Da Wasu Mutum 27 Kan Zargin Hakar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Jos
  • Nijeriya Ta Shigo Da Man Fetur Na Naira Tiriliyan 12 A 2024 – Rahoto
  • Sojoji Sun Miƙawa Gwamnatin Borno Mutane 75 Da Suka Ceto