Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-03-13@11:59:02 GMT

Ruwan Sama Ya Lalata Gidaje Da Makarantu A Jihar Kwara

Published: 13th, March 2025 GMT

Ruwan Sama Ya Lalata Gidaje Da Makarantu A Jihar Kwara

Sama da mutane 100 ne mazauna garin Ijagbo da ke karamar hukumar Oyun ta jihar Kwara suka rasa matsugunansu sakamakon ruwan sama ya yi barna a cikin al’umma.

 

Gidan Rediyon Najeriya ya tattaro cewa an lalata cibiyoyin ilimi da gidajen zama da rumfunan kasuwa tare da lalata dukiyoyi.

 

Guguwar ruwan sama ta yi barna a kwalejin Ansar Deen da ke Ijagbo yayin da ajujuwa sama da 10 suka yi lalace, inda dalibai da malamai suka makale.

 

An gano cewa guguwar ta afku ne da misalin karfe 4 na yamma. a ranar Litinin, tare da yaga rufin ajujuwan tare da lalata muhimman kayan koyo da kuma kawo cikas ga ayyukan ilimi.

 

Da suke Magana game da wannan ibdi’in, shugabannin makarantar, Mista Olaniyi Musbaudeen da Misis Saheed, sun yi kira ga gwamna AbdulRahman AbdulRazaq da ya gaggauta kawo musu tallafi domin dawo da ababen more rayuwa da suka lalace.

 

“Mun yi matukar bakin ciki da wannan bala’in. Rugujewar wadannan ajujuwa na haifar da babbar barazana ga karatun dalibanmu,” in ji Mista Musbaudeen.

 

A halin yanzu kwamishinan ilimi na jihar Kwara Dr Lawal Olohungbebe ya ziyarci makarantar da lamarin ya shafa domin tantance irin barnar da aka yi .

 

Ya kuma baiwa mahukuntan makarantun da sauran al’ummar jihar tabbacin shirin gwamnatin jihar na maido da kayayyakin da abin ya shafa.

 

COV/ALI MUHAMMAD RABIU

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Kwara Ruwan Sama

এছাড়াও পড়ুন:

Yemen zata sake kai hare-hare kan jiragen ruwan Isra’ila

Kasar Yemen ta sanar da cewa za ta ci gaba da kai hare-haren soji kan jiragen ruwan Isra’ila a wasu muhimman yankunan teku da ke gabar tekun kasar bayan cikar wa’adin da ta gindaya wa Isra’ila na ta sake bude mashigar zirin Gaza tare da bayar da damar kai agaji cikin yankunan Falasdinawa da yaki ya daidaita.

Rundunar sojin Yaman ta fitar da sanarwar a cikin daren jiya, inda ta ce za a ci gaba da kai hare-hare kan duk wasu jiragen ruwa masu alaka da ISra’ila kamar yadda Abdul-Malik al-Houthi shugaban kungiyar gwagwarmayar Ansarullah ta kasar ya bada umurni.

Tunda farko Shugaban kungiyar ta Ansarullah ya bai wa gwamnatin Isra’ila kwanaki hudu ta bude hanyoyin kai kayan agaji Gaza ko ta fuskanci martini.

Sanarwar ta kara da cewa “Wannan haramcin zai ci gaba da kasancewa har sai an sake bude hanyoyin shiga Zirin Gaza kuma an ba da izinin shigar da agajin jin kai da suka hada da abinci da magunguna.

A karshe sojojin sun jaddada goyon bayansu ga al’ummar Falasdinawa masu tsayin daka a yankin zirin Gaza da kuma gabar yammacin kogin Jordan da ke mamaye da su, wadanda kuma suka fuskanci mummunar ta’addancin Isra’ila, tare da jaddada goyon bayansu ga gwagwarmayar Falasdinawa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tambuwal Ya Raba Shinkafa Ga Gidaje Dubu 30 A Sokoto
  • An Bada Umarnin Sake Tsugunar Da Wadanda Harin ‘Yan Bindiga Ya Rutsa Da Su A Kebbi
  • Matashin da ke kera jiragen sama da bindigogi daga robobi
  • Yemen zata sake kai hare-hare kan jiragen ruwan Isra’ila
  • Zelensky ya je Saudiyya domin tattaunawar zaman lafiya
  • Harin Lakurawa: An Kashe Mutane 15 Tare Da Kona Kauyuka 7 A Birnin Kebbi
  • Gwamnatin Kano Ta Bullo Da Sabbin Hanyoyin Kare Makarantunta Daga Kalubalen Tsaro
  • Ko dai Gwamna Fubara ya yi murabus ko a tsige shi — APC
  • ‘Yan Sanda Sun Fara Bincike Kan Kisan Shugaban Kungiyar Miyetti Allah A Kwara