Cutuka Biyar Da Ake Ɗauka A Lokacin Zafi
Published: 13th, March 2025 GMT
Hukumar kula da yanayi ta Najeriya ta yi gargaɗi a baya-bayan nan dangane da ƙaruwar yanayin zafi a sassan ƙasar, yayin da jihohi da dama suke fuskantar ƙarin matsanancin zafi.
Gargaɗin ya kuma nuna cewa, tsananin zafin da za a yi fama da shi cikin kwanaki uku ko huɗu masu zuwa wanda zai haddasa damuwar da yanayin na zafi kan haifar a jihohi goma sha tara na ƙasar daga yankin arewa ta tsakiya da yankin gabashin ƙasar.
Kan haka ne muka tuntuɓi likita domin ya yi mana ƙarin bayani game da cututtuka biyar da aka fi kamuwa da su a lokacin zafi da kuma hanyoyin kare kai.
Sanƙarau – Dakta Hassan Ibrahim, likita a asibitin Biba da ke jihar Kaduna ya ce cutar sanƙarau na faruwa ne galibi idan aka samu cunkoson jama’a a wuri ɗaya da ya haɗu da zafi.
A cewarsa, “ƙwayoyin cuta za su shiga jikin mutum sai su shafi ƙwaƙwalwa sai a samu irin wannan.”
Zazzaɓin cizon sauro – Likitan ya ce idan yanayin zafi ya zo, mutane suna yawan buɗe jikinsu domin su sha iska. Ya ce “mutane sun fi zama a waje lokacin faɗuwar rana, lokacin da sauro ke tasiri da tafiyar da maleriya.
Hakan yana yawan taso da cutar maleriya a jikin mutane, kamar yadda likitan ya faɗa.
Fesowar ƙuraje – A lokacin zafi ne ake yawan zufa lamarin da ke janyo fesowar ƙuraje a jikn mutane wanda a cewar Dakta Hassan, idan ba a kula da su ba, “aka yi irin wata sosawa, yana iya kawo ciwo da wata ƙwayar cuta za ta iya ratsawa.”
Amai da gudawa – Dakta Hassan ya ce a irin wannan lokaci na zafi ne aka fi samun ƙuda da ruɓewar abinci. Ya ce idan ba a kula da abincin da muke ci ba, aka bari ƙuda suka yi damalmala a kai, hakan zai iya kawo ciwo a ciki idan aka ci.
Ƙonewar ruwa a jiki – A irin wannan yanayin, jikin mutum na yawan bushewa musamman a tsakanin dattijai. A cewar likitan, abin da ke sa mutum ya ji ƙishirwa, idan mutum na da rauni, ba za su samu jikinsu ya ankarar da su cewa su sha ruwa ba, ana so a riƙa shan ruwa a kai a kai.
Hanyoyin kariyaDakta Hassan Ibrahim ya ce muhimman matakan da ya kamata mutane su ɗauka wajen kare kansu daga kamuwa da cuta a lokacin zafi shi ne tabbatar da cewa ana samun yanayin “shiga da fita ta iska” ta hanyar buɗe taga a wuraren kwana da wuraren aiki da kuma rage cunkoson jama’a a wuri guda.
Ya kuma ce akwai buƙatar a riƙa amfani da gidan sauro idan za a kwanta domin kare kai daga kamuwa da cutar maleriya inda ya ce akwai buƙatar a taƙaita zama a waje da yamma.
A cewar likitan, babban matakin da ya kamata mutane su kiyaye shi ne na tabbatar da tsaftar abincin da za ake ci musamman ƴaƴan itatuwa da kuma tabbatar da tsaftar jiki.
Ƙarin wani matakin shi ne yawaita wanka a kai a kai domin rage yanayin zafi a jiki.
Sai kuma yawaita shan ruwa domin gujewa ƙonewar ruwa a jiki inda ya shawarci masu azumi da su yawaita shan ruwa da zarar sun yi buɗa baki.
Abin da ya sa aka fi kamuwa da cututtuka a yanayin zafiDakta Hassan Ibrahim ya bayyana cewa dalilin shi ne, galibin cututtuka sun fi haɓaka a lokacin zafi saboda yanayin tsaurin jiki da inda jiki ke tafiya.
“Jiki yana da yadda yake gyara kansa a duk yanayin da ya shiga, lokacin zafi yana zuwa masa da ƙarin matsi da yadda jikin zai fitar da zafi da inda zai riƙe daidai.” in ji likitan.
“A lokacin zafi, mun ƙara wa jikinmu aiki, saboda a ciki ɗumi gare shi kuma yana son ya riƙe ɗumi kuma a lokacin zafi, jikinmu yana ƙara aikin fitar da ɗumi waje yana kuma ƙoƙarin samun abin sanyi da zai iya daidaita yanayin da yake tafiyar da aikin.”
Likitan ya ce a irin wannan yanayi da jiki ke tsintar kansa a lokacin zafi, “akwai rauni da ke tasar da cutuka da za su yi tasiri.”
A cewar shi, kashi 90 na cututtuka a duniya yana da alaƙa da wani abu na sarari saboda akwai ƙwayoyin cuta da suka fi tasiri a yanayin zafi.
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Kariya Nijeriya yanayin zafi irin wannan
এছাড়াও পড়ুন:
Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [4]
Wannan umurni yana da tushen shari’a daga Alƙur’ani da Hadisi, kuma yana da hikima da fa’ida da dama. Allah Ta’ala Ya umurci Musulumi da yin isti’aza kafin karanta Alƙur’ani kamar yadda Ya labarta mana haka a cikin Suratul Nahli a aya ta 98. Inda Ya ce:” To idan za ka karanta Alƙur’ani sai ka nemi tsarin Allah daga Shaiɗan korarre (daga rahamar Allah).” Wannan aya ta tabbatar da neman tsarin Allah kafin a fara karatun Alƙur’ani.
Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [1] CIYARWA [Falalarta Da Muhimmancinta] Na 1Ma’anar Isti’aza:
Isti’aza na nufin neman tsari da kariya da fake wa a wurin Allah Shi kaɗai ban da waninsa daga sharrin Shaiɗan. Domin ƙarin haske duba Ibnu Jarir; Jãmi’ul Bayãni [1/111], Ibnu Kasir; Tafsirul Kur’anil Azim [1/27], da Ibnul Ƙayyim; Badã’i’ul Fawã’id [2/200].
Yaushe ake Isti‘aza?:
Malamai sun yi saɓani dangane da lokacinda za a yi Isti‘aza, sai dai magana mafi ingani da malamai mafiya yawa suke a kanta shi ne ana yin Isti‘aza ne kafin a fara karatu. Domin ƙarin haske duba Ibnu Ibnu Juzai; Kitãbut Tashīl fi Ulūmil Kitãbi [1/30], da Bagawī; Ma’ãlumut Tanzīli [[5/42] da Ibnu Aɗiyya; al-Muharrul Wajizi [1/58], da Ibnul Jauzi; Zãdul Masīri [1/14].
Hukunci Isti‘aza Kafin Karanta Alƙur’ani:
Malamai mafiya yawa sun tafi a kan mustahabbi ne yin isti‘aza a lokacin karanta Alƙur’ani a wajen salla. Amma sun yi saɓani a wajen karatun salla, an hakaitu Imamu Malik ba ya isti‘aza a sallar farilla amma yana yi a sallar asham, shi sa ake yi a sallar nafila. Amma Imam Abu Hanifa da Imam Asshafi’i suna yi isti‘aza a sallar farilla. Akwai waɗanda suke ganin wajibi ne a yi isti‘aza a salla gaba ɗaya. Domin ƙarin haske duba Kitãbu at-Tashīlu fi Ulūmi at-Tanzil [1/30] da Ibnu Kasir; Tafsirul Kur’anil Azim [1/26] da al-Ƙurɗubi; al-Jãmi’u Li’ahkãmil Ƙur’ãni [1/86]
Hikimar Yin Isti’aza Kafin Karanta Alƙur’ani:
Akwai hikimomi masu tarin yaw na yin isti‘aza kafin karatu. Ga wasu daga cikinsu:
1. Kariya daga tasirin Shaiɗan: Shaiɗan yana hana mutum fahimtar Alƙur’ani kuma yana kuma sanya ruɗani. Yin isti’aza na kare mai karatu daga fitinarsa.
2. Tsaftace zuciya: Isti’aza kafin karanta karanta Alƙur’ani yana ba wa zuciya tsarki da nufin Allah a karatu da samin tsoron Allah, tare da tadabburi.
3. Bin sunnon Annabi (SAW): Domin Annabi (SAW) yana Isti’aza kafin ya fara karatu.
4. Tsaftace Baki: Yin isti‘aza yana tsaftace baki daga abuwan da ta aikata na wargi da yasasshen zance, domin shiga karanta maganar Allah cikin tsarki da tsafta.
Daga: Abu Razina, Nuhu Ubale Paki
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp